BATUN WATAN SALLAH A NAJERIYA
Ta tabbata Ƙaramar Sallah za ta kama jibi Laraba, 01-10-1445 (Hijriyya), 10-04-2024 (Miladiyya) idan Allah Ya kai mu.
Wannan ya biyo sakamakon wata sanarwa daga Kwamitin Duban Wata na fadar Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III, cewa ba a ga watan Shawwal a yau Litinin ba.
Ke nan a bana al’ummar Musulmi a Najeriya za mu cika azumi zuwa kwana 30.
Muna roƙon Allah Ya nuna mana ranar lafiya, Ya amshi ibadojin da muka gabatar kuma Ya sa muna cikin ‘yantattun bayi, Amin.













