• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, April 16, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Ta'aziyya

TABBAS SHEIKH ABDUL’AZIZ DUTESEN TANSHI BAI “MUTU” BA

TA'AZIYYA

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
April 5, 2025
in Ta'aziyya
1
TABBAS SHEIKH ABDUL’AZIZ DUTESEN TANSHI BAI “MUTU” BA

Malam Idris Bai "Mutu" Ba

54
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

TABBAS SHEIKH ABDUL’AZIZ DUTESEN TANSHI BAI “MUTU” BA

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Malumfashi Mun Yi Babban Rashi

Malumfashi Mun Yi Babban Rashi

March 26, 2026
RAMADAN KARIM: 16-1447

Injiniya Tukur Hassan Tingilin (1978-2026)

March 5, 2026
Malam Idris Bai “Mutu” Ba

 

Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un!

An wayi gari a ranar Juma’a, 06-Shawwal-1446 (Hijiriyya) daidai da 04-Afirilu-2025 (Miladiyya) da babban labarin rasuwar fitaccen malamin Musulunci, Sheikh (Dokta) Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi. Kamar yadda labarin ya bayyana, malamin ya rasu ne a daren na Juma’a, a sakamakon wata rashin lafiya da ba a bayyana ba.

An gabatar da jana’izar Sheikh Abdul’aziz a filin Masallacin Idi na Games Village da ke Bauchi da misalin karfe 10 na safiyar Juma’a.

Dandazon mutane, a wajen jana’izar Dokta Idris

Wata majiya ta kusa da shi, wato Majalisin Dutsen Tanshi Bauchi, ta bayyana cewa malamin ya rasu yana furta Kalmar Shahada. Haka kuma cikin wasiyyar da ya bari, ta haɗa da cewa, ya hana ɗaukar hoto a yayin jana’izarsa. Ya hana zaman makoki a gidansa. Ya hana a riƙa kokawa wajen raka gawarsa zuwa maƙabarta, kamar kuma yadda ya ce, kada mutane su shiga maƙabarta da takalma.

Bayan wannan, shin jama’a ko kun san cewa tabbas Sheikh Idris bai “mutu” ba? Babu ko shakka, fitaccen malamin bai mutu ba. Babu shakka zai ci gaba da rayuwa a wannan duniya tamu. Kai bari in yi ta ta ƙare – Malam a yau ne ma zai ci gaba da da rayuwa tamkar yau aka haife shi.

Ga dalilan da suka sanya na faɗi cewa Malam bai “mutu” ba, duk kuwa da cewa a yau an binne gangar jikinsa a kabari.

Na farko dai, a Hadisi mai lamba 1631 na Sahih Muslim, an ruwaito cewa; Manzon Allah (saw) ya ce: “Idan mutum ya mutu, ayyukansa sun zo ƙarshe, illa abubuwa uku – sadaƙatul jariya, wato sadaka mai gudana, ilimi mai amfanin al’umma da kuma nagartaccen ɗa.”

Idan mun duba waɗannan abubuwa uku, Malam Abdul’aziz duk ya mallake su. Batun sadaƙatul jariya, Malam ya kafa makaranta wacce babu shakka za ta ci gaba da gudana har illa ma sha Allah.

Na biyu, batun ilimi, Dutsen Tanshi ya sadaukar da rayuwarsa wajen neman ilimin addinin Musulunci. Ya yi karatu a Jami’ar Madina, inda ya samu shaidar Digiri a fannin Shari’a. Haka kuma ya samu Digirin Digirgir a fannin Fikihu a Jami’ar Musulunci ta Sudan. Malam ya bayar da karatu, ya shayar da ɗalibai masu tarin yawa ilimi. Ya yi rubuce-rubuce masu tarin yawa a fagen Musulunci.

Ɗaya daga cikin litattafan da Dokta Idris ya rubuta

Na uku, Allah Ya albarkaci Malam Idris Abdul’aziz da nagartattun ‘ya’ya, waɗanda babu shakka za su riƙa yi masa addu’a.

Malam Idris zai ci gaba da rayuwa a duniyar nan, a zukatan miliyoyin nagartattun Musulmin duniya saboda ayyukansa na jaddada Musulunci da suka cika kafafen sadarwa na soshalmidiya.

Malam Abdul’aziz zai ci gaba da rayuwa a zukata da bakunan maƙiya Musulunci, musamman waɗanda ya riƙa yaƙa a zamanin da yake raye.

 

Babbar Makarantar da Dokta Idris ya gina

Babu shakka, Dokta Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi bai mutu ba. Zai ci gaba da rayuwa. Sunansa zai ci gaba da ƙwanƙwasa ƙofofi da zukata. Iliminsa da wa’azojinsa za su ci gaba da wanzuwa har illa ma sha Allah. A taƙaice, daga yau ma wasu dubban mutane za su fara saninsa da ayyukansa.

Muna roƙon Allah Ya ji ƙan shi da rahama. Ya yafe masa kurakurensa. Amin!
_______________
Bashir Yahuza Malumfashi, Editan Mujallar Taskar Gizago (online)
Juma’a 06-10-1446 (Hijiriyya)
04-04-2025 (Miladiyya).

Previous Post

Muhimman Batutuwan Dubawa A Littafin Tarihin IBB

Next Post

BANKWANA DA GWANI

Related Posts

Malumfashi Mun Yi Babban Rashi
Ta'aziyya

Malumfashi Mun Yi Babban Rashi

March 26, 2026
RAMADAN KARIM: 16-1447
Ta'aziyya

Injiniya Tukur Hassan Tingilin (1978-2026)

March 5, 2026
ALLAH JI ƘAN INJINIYA TUKUR
Ta'aziyya

ALLAH JI ƘAN INJINIYA TUKUR

February 27, 2026
Next Post
BANKWANA DA GWANI

BANKWANA DA GWANI

Comments 1

  1. Guna niyoss pkm says:
    10 months ago

    Tabbas malam yarasu amma kuma kamar yana raye sbd ayyukansa nabada shidima ga al umma sunanann sunata tfy kmr malam yn raye
    ina mika ta azziya daganan garin potiskum Allah yjkn malam

    Reply

Leave a Reply to Guna niyoss pkm Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

BATUN SASANCI DA ‘YAN BINDIGA A JIHAR KATSINA

BATUN SASANCI DA ‘YAN BINDIGA A JIHAR KATSINA

September 15, 2025
TSOKACINMU NA YAU (22)

TSOKACINMU NA YAU (22)

March 22, 2025
Digirin Girmamawa: Ya Kamata Jami’o’in Najeriya Su Karrama Rarara

Digirin Girmamawa: Ya Kamata Jami’o’in Najeriya Su Karrama Rarara

September 21, 2025
Rusau A Kano: Ja’afar-Ja’afar Ya Soki Rusa Hasumiyar Algaita

Rusau A Kano: Ja’afar-Ja’afar Ya Soki Rusa Hasumiyar Algaita

June 14, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa
  • Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye
  • Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

April 16, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.