TSOKACINMU NA YAU (22)
Yau Asabar, 22-Ramadan-1446, Hijirar Manzon Allah (saw), wacce ta yi daidai da 22-Maris-2025, Miladiyya.
Yau za mu yi tsokaci ne game da mummunar halayyar HASSADA. Babu shakka ita hassada, muninta ya wuce duk inda ake tunani, domin kuwa ita ce halayyar da ta sabbaba wa shaiɗan tsinuwar Allah da taɓewa.
Kamar yadda masu hikima suka ce, hassada ga mai rabo taki ce. To mai hassada yana faɗa ne da da ƙudurar Allah, wanda a sanadiyyar haka zai kasance cikin baƙin ciki da rashin natsuwa; domin yana gani wanda yake wa hassada zai ta ci gaba, shi kuwa yana dakon baƙin ciki.
Lallai ne mu kiyayi kanmu daga hassada,
ko don mu zauna lafiya.
Allah sa mu dace, Amin.
Mu wuni lafiya.
Naku,
Bashir Yahuza Malumfashi,
Editan Mujallar Taskar Gizago.












