TSOKACINMU NA YAU (16)
Yau Lahadi, 16-Ramadan-1446, Hijirar Manzon Allah (saw), wacce ta yi daidai da 16-Maris-2025, Miladiyya.
Tsokacinmu na yau a kan AMANA ne. A baya mun yi magana game da gaskiya da adalci, to amana na ɗaya daga cikin turke na uku a jerin kyawawan halaye da ɗabi’un da ke taimakon al’umma.
Duk wata musharaƙa da za ta haɗa ka da wani ɗan Adam, to amana ce. Don haka riƙe ta da gudanar da ita bisa dacewa, shi ne abin bukata.
Lallai ne mu zama masu riƙon amana a dukkan lamurranmu na rayuwa – sana’a ce, aiki ne da dukkan wata musharaƙa ta zamantakewar rayuwa. Amana gonar Allah ce, babu alheri a tozarta ta.
Allah sa mu dace, Amin.
Mu wuni lafiya.
Naku,
Bashir Yahuza Malumfashi,
Editan Mujallar Taskar Gizago.












