• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Sunday, April 26, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Labarai

KO YANZU ZA A IYA FARA KARATU A BABBAR KWALEJIN NOMA TA NABANJE – Malam Labiru Ƙafur

TATTAUNAWA

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
August 5, 2025
in Labarai
0
KO YANZU ZA A IYA FARA KARATU A BABBAR KWALEJIN NOMA TA NABANJE – Malam Labiru Ƙafur

Malam Labiru Musa Ƙafur, mni

44
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

KO YANZU ZA A IYA FARA KARATU A BABBAR KWALEJIN NOMA TA NABANJE – Malam Labiru Ƙafur

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
A hagu: Hon. Alhaji Kabir Ibrahim Masari ne, yayin da yake amsar takardar tabbatar da kafa makarantar Federal College of Agriculture & Technology, Nabanje daga hannun Ministar Ilimi, Farfesa Suwaiba Sa’id Ahmad

 

A kwanakin baya, Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar da kafa Kwalejin Noma Da Ƙere-Ƙere a garin Nabanje, Ƙaramar Hukumar Ƙafur, Jihar Katsina. A tattaunawarmu da ɗaya daga cikin mambobin hukumar gudanarwar kwalejin, Malam Labiru Musa Ƙafur, mni, ya bayyana cewa za a iya fara karatu a makarantar, tun kafin a kammala gina mazauninta, sannan ya fayyace irin fa’idojin da al’umma za su samu daga wannan babbar makaranta da aka samu a yankin. Ga yadda tattaunawar ta kasance:

TG: Za mu so ka yi mana bayani a taƙaice game da wannan babbar makaranta ta koyar da noma da ƙere-kere.

Malam Labiru: Da farko dai, kamar yadda ka sani, ina ɗaya daga cikin mambobin hukumar gudanarwa ta wannan makaranta mai suna Federal College of Agriculture & Technology. Mai girma Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, GCFR ya naɗa mu. Ita wannan makaranta ta Gwamnatin Tarayya ce. An samar da ita ce da nufin a riƙa koyar da harkokin noma, kiwo da kimiyya da ƙere-keren abubuwan da suka danganci wannan harka. Haka kuma akwai batun ilimin sarrafa abinci da sauransu.

TG: Ashe makarantar tana da faɗi haka?

Malam Labiru: Lallai kam, kasancewarta ta gaba da sakandare, makarantar babba ce. Ba kawai harkar noma tsuransa za a tsaya ba, shi ya sanya aka kira ta da sunan Federal College of Agriculture & Technology. Akwai wasu tsarin ayyuka da sana’o’i waɗanda suka jiɓinci noma, kamar sarrafa kayan gona, ƙera kayan aikin gona da sauransu. Wannan makaranta tana nan a ƙauyen Nabanje, kilomita 4 ne daga garin Ƙafur, a kan hanyar Zariya. Kamar dai yadda aka kafa Federal Polytechnic ta Efuru, wacce ta ta’allaƙa ga kimiyyar mai da iskar gas, to ita wannan ta danganci noma da kiwo da dangoginsu.

TG: Ita wannan an kafa ta don bunƙasa noma a Arewa ke nan?

Malam Labiru: Haka ne, kasancewar Arewa, nan ne harkokin noma da kiwo suke da ƙarfi. Don haka wannan makaranta, za ta amfani al’ummar Ƙafur da kewaye da Jihar Katsina da Arewa, da ma Najeriya baki ɗaya ta fuskar koya fasahar noma da kiwo na zamani kuma a ilimance, domin bunƙasa ƙasa da abinci da samar da ayyukan yi da sana’o’i.

Malam Labiru Musa Ƙafur, mni

TG: Ko akwai wani shiri na fara karatu da sauri a makarantar, duk da cewa ba a gama gina mazauninta na dindindin ba?

Malam Labiru: Fatanmu ne mu ga makarantar ta fara aiki nan ba da daɗewa ba. Ka san ba za ta fara ba, har sai hukumomin da ke kula da al’amarin sun ba da izinin haka. Amma akwai wuraren da suka dace na wucingadi da za a iya fara karatu, idan an ba da izinin. A nan ƙauyen Nabanje, akwai wata makarantar koyon sana’o’i (Skills Acquisition Centre), akwai asibiti babba, wanda ba a fara aiki da shi ba, akwai makarantar sakandaren rana-rana. Duk waɗannan wuraren, za a iya amfani da su domin fara karatu, kafin kammala ginin makarantar na dindindin. Kuma shi Hon. Ibrahim Kabir Masari, akwai wuraren da zai iya tanada a cikin garin Masari da Ƙafur, domin samar da gidajen kwana ga malamai, na wucin-gadi, kafin makarantar ta samu nata.

Kuma koda za a fara yanzu, babu wata damuwa. Ya zuwa yanzu dai Hukumar NBTC (mai kula da kwalejijin kimiyya da ƙere-kere) sun zo har karo biyu, sun duba wuraren da na gaya maka. Kuma sun gamsu da cewa za a iya fara karatu. Haka su ma jami’an gudanarwa sun zo sun duba kuma sun ce lallai za a iya fara karatu a wuraren na wucin-gadi. Yanzu abin da kawai ake jira, shi ne hukumomin da ke da ikon ba da izini da kuma kuɗin gudanarwa daga Gwamnatin Tarayya.

TG: Wane irin muhimmanci ya kamata al’ummar Yankin Karaɗuwa ya kamata su ba wannan makaranta?

Malam Labiru: Kamar yadda ka faɗa, ya kamata mutane su san cewa, wannan makaranta ta Gwamnatin Tarayya ce, don haka ta ‘yan Najeriya ce baki ɗaya. Ke nan ɗan ƙasa zai iya zuwa daga kowane yanki yake. Amma dai ai an ce da arziƙi a garin wasu, gara a ce garinku ne. Don haka ina kira ga al’ummarnu da su shirya amsar baƙi daga dukkan sassan ƙasar nan. Hakan ma kaɗai zai bunƙasa yankin namu, baya ga sauran abubuwan amfani marasa adadi.

TG: A faɗaɗa mana bayani, yallaɓai.

Malam Labiru: Kamar yadda na ce, wannan makaranta ta kowa ce a Najeriya. Ta fannin ɗaukar ma’aikata da ɗalibai da sauransu, za a duba cancanta ne da dacewa, domin nagarta ake so da biyan buƙata domin bunƙasa al’umma ta fannin noma da kiwo da sana’o’in da suka dangance su, amma kasancewar a nan yankin take, lallai akwai wani tagomashi na musamman da al’ummarmu za su samu mai yawa. Misali, hatta ta fannin sana’o’i da ayyukan yi za su ƙaru a wannan yanki, albarkacin makarantar nan, domin baƙi za su shigo daga sassa daban-daban.

Mai ba Shugaban Ƙasa Shawara ta Fuskar Siyasa, Hon. Alhaji Kabir Ibrahim Masari da Ministar Ilimi, Farfesa Suwaiba Sa’id Ahmad da sauran membobin hukumar gudanarwa na Federal College of Agriculture & Technology, Nabanje, jim kaɗan da ƙaddamar da su a Abuja, kwanakin baya

Kuma ina ba da shawara da cewa mu ba da haɗin kai da goyon baya, ta yadda al’amarin zai amfane mu sosai. Kada mu damu da cewa dole sai wane ɗan nan zai zama shugaba kaza da kaza. Abin da ake buƙata shi ne bin doka da oda da ƙa’ida. Zan ba ka misali da Jami’ar Ahmadu Bello Zariya. Lokacin da aka gina ta, Sardauna Ahmadu Bello, daga ƙasar Newzealand ya ɗauko VC (Shugaban Jami’a), ba ma daga Ingila ba, wacce ita ce uwa ga Najeriya a lokacin. Wannan ke nuna, madamar mutum ya cancanta kuma zai bayar da abin da ake bukata da nagarta, to babu damuwa da inda ya fito. Muna fatan dai a samu nasara, yaranmu su samu ilimi, al’ummarmu ta samu cigaba, ƙasarmu ta bunƙasa da arziƙin noma da kiwo da sauransu.
_______________

Previous Post

INSECURITY IN NORTHERN NIGERIA: AN OPEN LETTER TO NSA NUHU RIBADU

Next Post

TAƁARƁAREWAR TSARO A AREWA: BUƊAƊƊIYAR WASIƘA ZUWA GA MALAM NUHU RIBADU

Related Posts

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi
Labarai

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Labarai

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina
Labarai

Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina

February 13, 2026
Next Post
INSECURITY IN NORTHERN NIGERIA: AN OPEN LETTER TO NSA NUHU RIBADU

TAƁARƁAREWAR TSARO A AREWA: BUƊAƊƊIYAR WASIƘA ZUWA GA MALAM NUHU RIBADU

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Wike Sent Heads of FCT Agencies, Parastatals Packing

Wike Sent Heads of FCT Agencies, Parastatals Packing

September 28, 2023
ACF to TINUBU: MR. PRESIDENT, YOUR GOVERNMENT NEGLECTS AND SIDELINES AREWA

ACF to TINUBU: MR. PRESIDENT, YOUR GOVERNMENT NEGLECTS AND SIDELINES AREWA

August 1, 2025
RAPED SOUL

RAPED SOUL

November 26, 2024
Happy Birthday Sir: A Tribute to Malam Labiru Musa Ƙafur

Happy Birthday Sir: A Tribute to Malam Labiru Musa Ƙafur

October 28, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Duniya Ba Gidan Zama Ba
  • Minista Dr. Muttaqha Rabe Darma Kana Bi Na Bashi
  • Governor Dikko Radda Commissions Community Development Projects Built by Muntari Sagir in Malumfashi

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Duniya Ba Gidan Zama Ba

Duniya Ba Gidan Zama Ba

April 24, 2026
Minista Dr. Muttaqha Rabe Darma Kana Bi Na Bashi

Minista Dr. Muttaqha Rabe Darma Kana Bi Na Bashi

April 22, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.