TSOKACINMU NA YAU (17)
Yau Litinin, 17-Ramadan-1446, Hijirar Manzon Allah (saw), wacce ta yi daidai da 17-Maris-2025, Miladiyya.
A yau za mu tattauna ne game da ADDINI. Babban abin da ya kamata mu fahimta kuma mu sanya a ranmu shi ne, addini hanya ce ta bautar Allah ko kuma duk wani abin bauta da “mutum” ya yarda da shi.
Addini zaɓi ne na mutum. Babu tilas a kansa. Ke nan, babban abin da yake almuhim shi ne, mu zama masu kiyayewa da daraja zaɓin juna.
Musulmi, Kirista ko Bayahude ko mai addinin gargajiya, kowa ya tsaya matsayinsa. Mu guji yin kutse ko wulaƙanta juna bisa fahimtar zaɓinmu na addini. Idan tattaunawa ta kama mu, mu yi ta cikin fahimta da daraja juna.
Allah sa mu dace, Amin.
Mu wuni lafiya.
Naku,
Bashir Yahuza Malumfashi,
Editan Mujallar Taskar Gizago.













