TSOKACINMU NA YAU (15)
Yau Asabar, 15-Ramadan-1446, Hijirar Manzon Allah (saw), wacce ta yi daidai da 15-Maris-2025, Miladiyya.
A tsokacinmu na yau, za mu duba batutuwa game da Adalci. Shi dai adalci na nufin ajiye kowane abu a daidai gurbin da ya dace da shi. Ma’ana, bayar da haƙƙi ga mai haƙki – babu ciri babu coge, in ji ta ‘yan caca.
A matsayinmu na mutane, daidai ne mu zama adalai a duk matsayin da muka samu kanmu. Kai shugaba ne, maigida ko ke uwargida ce; ɗan kasuwa ne, malami ko ɗalibi? Kowa na buƙatar ka yi masa adalci a kowace mu’amala, domin kuwa da adalci ne rayuwa za ta daidaita, a samu lafiya da zaman lafiya da ci gaba.
Allah sa mu dace, Amin.
Mu wuni lafiya.
Naku,
Bashir Yahuza Malumfashi,
Editan Mujallar Taskar Gizago.













