• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, January 16, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Addini

Aure Sunnar Manzo (saw): Isma’il Angon A’isha

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
October 31, 2025
in Addini
0
Aure Sunnar Manzo (saw): Isma’il Angon A’isha

Isma'il Sanda Angon A'isha

60
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Aure Sunnar Manzo (saw): Isma’il Angon A’isha

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Baffa Hotoro Ka Ci Amanar Ilimi

Baffa Hotoro Ka Ci Amanar Ilimi

November 29, 2025
Jama’a Mu Fahimta: Musulunci Daban Ƙungiyanci Daban

Jama’a Mu Fahimta: Musulunci Daban Ƙungiyanci Daban

November 28, 2025
Isma’il Sanda Angon A’isha

                           •••••••
Allah (swt) a cikin Suratun Nur, aya ta 32 yana cewa: “Ku yi aure da waɗanda suke daga cikinku maza da mata masu ɗabi’a nagari. Idan kuwa su talakawa ne, Allah zai wadatar da su daga falalarsa.”

Haka kuma Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Aure rabin addini ne. Wanda ya yi aure, ya cika rabin addininsa, sai ya ji tsoron Allah a sauran rabin.”

A aya da hadisin da suka gabata, suna nuna yadda aure yake da daraja a Musulunci, kasancewarsa hanya ta tsaftace rayuwa, tsare imani da kuma gina al’umma mai ƙarko.

A gobe Asabar, idan Allah ya kai mu lafiya, za mu shaida auren ɗan uwa mai albarka, Malam Isma’il A. Sanda, wanda ya rungumi wannan sunna ta aure.

Isma’il matashi ne mai haƙuri, dattako da girmama manya. Mutum ne da ke da kyakkyawar mu’amala da mutane. Yana da zumunci da hali na natsuwa da ladabi. Ya tashi cikin tarbiyyar iyaye nagari, abin da ya bayyana a cikin yadda yake hulɗa da jama’a cikin tawali’u da kamala.

Aure ba kawai haɗin jiki ba ne, haɗin zuciya ne da niyya mai tsafta. A matsayinka na sabon ango, Malam Isma’il ya kamata ka fahimci cewa zaman aure yana buƙatar haƙuri, juriya da yarda da juna. A’isha ita ce abokiyar rayuwarka yanzu, wadda za ta kasance mataimakiyarka wajen bauta wa Allah da gina iyali masu albarka. Ya kamata ka riƙe ta da ƙauna da girmamawa, kamar yadda Manzon Allah (SAW) ya yi wa matansa.

Haka nan ya zama wajibi ga amarya A’isha, da ki kasance mace mai biyayya, mai tawali’u da kula da mijinki da gidansa. Aure na buƙatar tausayawa da fahimta. A duk lokacin da ɗayanku ya yi kuskure, ɗayan ya gafarta wa ɗaya, domin rayuwa ta ci gaba cikin farin ciki.

A dukkanin rayuwar aure, ana buƙatar addu’a da neman taimakon Allah. Isma’il da A’isha, ku kasance masu yawaita istighfari. Ku yawaita sallolin nafila. Ku lizimci karanta Alƙur’ani a gidanku, domin hasken gida shi ne ibada. Idan aure ya ginu a kan addini da haƙuri, to farin ciki da albarka ba za su taɓa ƙarewa ba a iyalinku.

A wannan gaɓar, a madadin ni Bashir Yahuza Malumfashi (Fasihin Galadiman Katsina-I) da iyalina, ‘yan uwa da abokan arziƙi, muna yi wa sabon ango Malam Isma’il Sanda da amaryarsa A’isha fatan alheri da zaman lafiya. Allah Ya sa wannan aure ya zama tushen rahama, soyayya da albarka, ya ba ku zuri’a tagari, ya kare ku daga shaiɗan da fitina. Amin-Summa-Amin.
_______________

Previous Post

Daura Gidan Tarihin Hausa

Next Post

Tsakanin A’isha Humaira da Umar Baana: Sulhu Alheri Ne

Related Posts

Baffa Hotoro Ka Ci Amanar Ilimi
Addini

Baffa Hotoro Ka Ci Amanar Ilimi

November 29, 2025
Jama’a Mu Fahimta: Musulunci Daban Ƙungiyanci Daban
Adabi

Jama’a Mu Fahimta: Musulunci Daban Ƙungiyanci Daban

November 28, 2025
Muhammadu (Saw): Haske Mai Haskakawa
Addini

Muhammadu (Saw): Haske Mai Haskakawa

November 21, 2025
Next Post
Tsakanin A’isha Humaira da Umar Baana: Sulhu Alheri Ne

Tsakanin A’isha Humaira da Umar Baana: Sulhu Alheri Ne

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Za Mu Tunkari Matsalolin Ruwa Da Gaske A Jihar Katsina – Injiniya Tukur

Za Mu Tunkari Matsalolin Ruwa Da Gaske A Jihar Katsina – Injiniya Tukur

July 17, 2023
Rusau A Kano: Ina Bayan Gwamna Abba Gida-Gida

Rusau A Kano: Ina Bayan Gwamna Abba Gida-Gida

June 4, 2023
TATTAUNAWAR KHALID IMAM: Zuwa Ga Malam Bashir

TATTAUNAWAR KHALID IMAM: Zuwa Ga Malam Bashir

October 22, 2023
Shugaban INEC ya gargaɗi ma’aikata su yi aiki da gaskiya a zaɓen gwamnonin Bayelsa, Imo da Kogi

Shugaban INEC ya gargaɗi ma’aikata su yi aiki da gaskiya a zaɓen gwamnonin Bayelsa, Imo da Kogi

November 6, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation
  • Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco
  • Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

January 15, 2026
Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

January 14, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.