Aure Sunnar Manzo (saw): Isma’il Angon A’isha
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

•••••••
Allah (swt) a cikin Suratun Nur, aya ta 32 yana cewa: “Ku yi aure da waɗanda suke daga cikinku maza da mata masu ɗabi’a nagari. Idan kuwa su talakawa ne, Allah zai wadatar da su daga falalarsa.”
Haka kuma Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Aure rabin addini ne. Wanda ya yi aure, ya cika rabin addininsa, sai ya ji tsoron Allah a sauran rabin.”
A aya da hadisin da suka gabata, suna nuna yadda aure yake da daraja a Musulunci, kasancewarsa hanya ta tsaftace rayuwa, tsare imani da kuma gina al’umma mai ƙarko.
A gobe Asabar, idan Allah ya kai mu lafiya, za mu shaida auren ɗan uwa mai albarka, Malam Isma’il A. Sanda, wanda ya rungumi wannan sunna ta aure.
Isma’il matashi ne mai haƙuri, dattako da girmama manya. Mutum ne da ke da kyakkyawar mu’amala da mutane. Yana da zumunci da hali na natsuwa da ladabi. Ya tashi cikin tarbiyyar iyaye nagari, abin da ya bayyana a cikin yadda yake hulɗa da jama’a cikin tawali’u da kamala.
Aure ba kawai haɗin jiki ba ne, haɗin zuciya ne da niyya mai tsafta. A matsayinka na sabon ango, Malam Isma’il ya kamata ka fahimci cewa zaman aure yana buƙatar haƙuri, juriya da yarda da juna. A’isha ita ce abokiyar rayuwarka yanzu, wadda za ta kasance mataimakiyarka wajen bauta wa Allah da gina iyali masu albarka. Ya kamata ka riƙe ta da ƙauna da girmamawa, kamar yadda Manzon Allah (SAW) ya yi wa matansa.
Haka nan ya zama wajibi ga amarya A’isha, da ki kasance mace mai biyayya, mai tawali’u da kula da mijinki da gidansa. Aure na buƙatar tausayawa da fahimta. A duk lokacin da ɗayanku ya yi kuskure, ɗayan ya gafarta wa ɗaya, domin rayuwa ta ci gaba cikin farin ciki.
A dukkanin rayuwar aure, ana buƙatar addu’a da neman taimakon Allah. Isma’il da A’isha, ku kasance masu yawaita istighfari. Ku yawaita sallolin nafila. Ku lizimci karanta Alƙur’ani a gidanku, domin hasken gida shi ne ibada. Idan aure ya ginu a kan addini da haƙuri, to farin ciki da albarka ba za su taɓa ƙarewa ba a iyalinku.
A wannan gaɓar, a madadin ni Bashir Yahuza Malumfashi (Fasihin Galadiman Katsina-I) da iyalina, ‘yan uwa da abokan arziƙi, muna yi wa sabon ango Malam Isma’il Sanda da amaryarsa A’isha fatan alheri da zaman lafiya. Allah Ya sa wannan aure ya zama tushen rahama, soyayya da albarka, ya ba ku zuri’a tagari, ya kare ku daga shaiɗan da fitina. Amin-Summa-Amin.
_______________













