SIYASAR NIGERIA: Tattaunawar Aminu Waziri Da Baturen Ingila

Malam Aminu Waziri ya ce, “wani abokina Bature kuma Ɗan Majalisa a ƙasar Ingila, muna tattaunawa da shi – domin ya faye bin diddigin harkokin siyaysa da dimokuraɗiyyar Najeriya. Kusan duk abubuwan da suke faruwa, yana bibiya. Shi ne ya yi mani wata tambaya cewa:
“Abbokina, me ya sa na ga kusan duk lokacin da aka yi zaɓen ƙananan hukumomi, kamar jam’iyyar gwamnatin da ke mulki a wannan jihar, ita ke cinye zaɓen ɗari bisa ɗari?”
Na ce masa “e, gaskiya haka ne. Domin duk jama’iyyar da ke mulki, ita ke da iko da hukumar zaɓe ta jihar kuma yadda gwamnatin ke so a yi; haka za a yi… kuma duk da ratsuwar da gwamnan da jami’an hukumar suka yi, lallai ba zai canza komi ba.”
Malam Aminu ya ce, “jin haka sai abokin nawa Bature ya yi tagumi, ya yi shiru, ya yi ajiyar zuciya. Ya ƙara ce mani:
“Kuma ana kashe kuɗaɗe a wurin yin hakan?”
Na ce masa sosai kuwa… Sai ya ce mani:
“Ai kam da za ku gane, maimakon ku kashe kuɗi masu yawa wurin gudanar da zaɓen gangan na ƙananan hukumomi, wataƙila kuɗin za su iya yi maku amfani wurin wasu ayyukan more rayuwa, ko na jin kan al’umma; ai har gwara ku dinga naɗa “KANTOMOMI” yadda ba sai an kashe makudan kuɗi ba.”
Malam Waziri ya amsa masa da cewa: “Ni kam na ce masa ai Doka ba ta amince da hakan ba.
“Daga nan sai abokin nawa Bature ya yi tagumi cikin mamaki, bai sake magana ba!”
_______________
Malam Aminu Waziri ɗan siyasa ne kuma Ƙwararre a harkar gine-gine. Ya wallafa wannan tattaunawa a shafinsa na Facebook













