• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Sunday, May 3, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Labarai

Kafafen Yaɗa Labarai Su Ne Manyan Dirkokin Da Ke Ɗauke Da Nagartacciyar Dimokiraɗiyyarmu – Minista

Daga Wakilinmu by Daga Wakilinmu
December 20, 2023
in Labarai
0
Kafafen Yaɗa Labarai Su Ne Manyan Dirkokin Da Ke Ɗauke Da Nagartacciyar Dimokiraɗiyyarmu – Minista

Minista Idris (a dama) tare da maziyartan daga IPI

10
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Kafafen Yaɗa Labarai Su Ne Manyan Dirkokin Da Ke Ɗauke Da Nagartacciyar Dimokiraɗiyyarmu – Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya sake jaddada ƙudirin wannan gwamnati wajen bai wa kafafen yaɗa labarai ‘yancin su, ba tare da takunkumi ko dabaibayi ba.

Related posts

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026

Ya ce kafafen yaɗa labarai sun taka muhimmiyar wajen tabbatar da kafuwar turakun dimokiraɗiyyar ƙasar nan, don haka abu ne da ya zama dole a a yi riƙo da kafafen yaɗa labarai saboda tasirin su.

Ministan ya bayyana haka ne a ranar Talata, lokacin da ya karɓi baƙuncin shugabannin Cibiyar Kare Haƙƙin Jaridu da ‘Yan Jarida ta Duniya (IPI), a ƙarƙashin shugaban ta, kuma Babban Editan jaridar Premium Times, Alhaji Musikilu Mojeed.

IPI ta kai ziyara ne a ranar Talata, 19 ta Disamba, a ofishin ministan da ke Abuja.

IPI ƙungiya ce ta manyan editocin jaridu na duniya, masu kafafen yaɗa labarai da kuma fitattun ‘yan jarida.

Babban dalilin kafa ƙungiyar shi ne kare haƙƙin aikin jarida tare da tsayawa kan kare aikin jarida da ‘yan jarida daga dukkan wata barazanar da ka iya tunkarar su.

Ministan ya ƙara nanata matsayar Shugaba Tinubu dangane da ‘yancin kafafen yaɗa labarai, tare da cewa shi kan sa shugaban tsohon ɗan gwagwarmayar kare ‘yancin dimokiraɗiyya ne, don haka ya na da dukkan ruwa da tsaki wajen nuna goyon bayan ‘yancin kafafen yaɗa labarai da ‘yan jarida.

Kuma ya yi alƙawari cewa gwamnatin sa ba za ta taɓa yi wa aikin jarida ƙarfa-ƙarfa ba.

Idris ya ce dimokiraɗiyya a Nijeriya na buƙatar nagartacciyar alƙibla, wadda kuma gwamnati ke neman gudunmawar dukkan masu karsashin ƙara mata nagarta, ciki kuwa har da jaridu, kafafen yaɗa labarai da ‘yan jarida su kan su.

Ya ce yi wa wannan tsari garambawul nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa da kowa, a dunƙule.

Daga nan ya yi yabo da jinjina ga shugaban IPI dangane da zaɓen sa da aka yi ya jagoranci cibiyar.

Ya yi kira ga Mojeed da ya yi amfani da ƙwarewar sa ta aikin jarida wajen yi wa IPI kyakkyawan jagoranci.

Tun da farko, sai da Shugaban na IPI, Musikilu Mojeed, ya shaida wa ministan cewa a yanzu ana samun cigaba a farfajiyar kafafen yaɗa labarai, don haka ana yi wa aikin jarida kyakkyawar fata nagari.

Daga nan ya yi kira ga gwamnati da ta tabbatar da kare rayuka da lafiyar ‘yan jarida a duk inda suke aiki.

Ya kuma tabbatar wa da Idris cewa IPI za ta ba shi goyon baya, musamman kasancewa ya na ɗaya daga cikin membobin farko da su ka kafa cibiyar.

Previous Post

INEC Za Ta Gudanar Da Zaɓuɓɓukan Da Kotu Ta Soke Da Na Cike Gurabu 34 A Fabrairu 2024 – Yakubu

Next Post

Minista Ga VON: Ku Yaɗa Kyawawan Labaran Nijeriya Ga Duniya

Related Posts

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi
Labarai

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Labarai

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina
Labarai

Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina

February 13, 2026
Next Post
Minista Ga VON: Ku Yaɗa Kyawawan Labaran Nijeriya Ga Duniya

Minista Ga VON: Ku Yaɗa Kyawawan Labaran Nijeriya Ga Duniya

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

TABBAS SHEIKH ABDUL’AZIZ DUTESEN TANSHI BAI “MUTU” BA

TABBAS SHEIKH ABDUL’AZIZ DUTESEN TANSHI BAI “MUTU” BA

April 5, 2025
Yunƙurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (15)

Yunƙurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (15)

March 23, 2026
Kasafin 2024 Ya Fitfita Jaddada Ajandar Sassaita Nijeriya – Idris

BADAƘALAR NAIRA MILIYAN 585: Gwamnati Ta Fara Binciken Ministar Agaji – Idris

January 8, 2024
Hajia Amina Donates Mosque Building to Muslim Community

Hajia Amina Donates Mosque Building to Muslim Community

March 11, 2024

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana
  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)
  • General Buratai (A Poem)

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

April 28, 2026
Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

April 27, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.