• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, April 16, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Adabi

Ziyara Biu

WAƘE

Khalid Imam by Khalid Imam
May 11, 2024
in Adabi
0
Visit to Biu

Mai Martaba Sarkin Biu da Ayarinsa

13
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Ziyara Biu

(Wake)

Related posts

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

April 11, 2026
FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

March 7, 2026

Khalid Imam

*****

Malam Khalid Imam malamin makaranta kuma marubuci ne ya bar Kano mazaunin sa ranar 9 ga watan Afirlu, 2024 ya kai ziyara a Birnin Biu har ranar 12 ga watan Afirlu, 2024. Waɗannan waƙoƙi biyu, ya ƙaga su a lokacin Ƙaramar Sallar Ramadan, a ranar 11 ga watan Afirlu, 2024. Daga baya ya juya waƙoƙin a cikin Turanci

*****

Daga Hagu: Betaran Biu, Janar TY Buratai (mai ritaya), Mai Martaba Sarkin Biu da kuma Dokta Bukar Usman, OON

Na je Biu na yi Salla,
Ƙarama a cikin karamci,
Mutane masu kirki,
Mutumci ga zumunci.

Na je salla ta Idi,
Mun yi Idi har da sarki,
Difiti Gwamna na Borno,
Ya zo Salla gidansu.

Mutan Biu sun ga nasu,
Ya zo domin su gaisa,
Mata da maza da yara,
Sun yi murna sun ga ɗansu.

Kowa murna yake yi.
Sarki duka Hakimansa,
Sun hau doki da kansu,
Ana ta kiɗa da busa.

Ƙasar Biu na da kyawu.
Biu birni ce a tsauni,
Bishiyar tsauni halinta,
Dogon rai ne gare ta.

Na ga al’adu na dauri,
Masu adana tarihin Biu,
Masu bayyana martabarta,
Masu nuna farin jininta.

Masu bayyana tarihinta,
Masu nuna irin ƙawarta,
Jarumanta juriyarta
A Hawan Salla na gan su

Na je Biu gaida dangi,
Na Bukar Usmanu giwa,
Bukar Usmanu Dokta,
Mai gida ne ni gare ni.

Kogi bishiya halinsu,
Alheri ba su rowa,
Kogi zai ba ka kifi,
Ruwan sha ko na noma.

Bishiya ko ta ba ka ‘ya’ya,
Inuwar hutu ka huta,
Bukar Usmanu tabbas,
Bishiya ne ga shi kogi.

Bukar kishi gare shi,
Ya yi banki nan garinsu,
Bankinsa na al’umma ne,
Burinsa ya ba da jari.

Jarin sana’a da noma,
Mutan Biu duk su samu,
Rijiyoyi yai na bohol,
Shekaru sun kai talatin.

Duk don jama’a su rayu,
Cikin sauƙi wadata,
Sai mai kishi na dangi,
Ke kai jari garinsu

Na ga yadda ake zumunci,
A ƙasar Biu babu bare,
‘Yan uwa ne su ga juna,
Noma ba sa kasala.

Tallafin ƙaro karatu,
Bukar na ba wa dangi,
Bukar na ba maƙota
Tallafi na iri da taki.

Wanda ke jinya a dangi,
Ko maƙota bai barin shi,
Magani da kuɗin buƙatu,
Bukar na bai wa kowa.

Na je na gaida Sarki,
Sarkin Biu jarumi,
Zaki shi ke da iko,
A daji ba kamarsa.

Sarkin Biu gun karamci,
Jinjina tilas gare shi,
Ya san daraja ta baki,
Ni shaida ne Khalidu.

Sarkin Biu na da kyauta,
Ga alfarama da hira,
Fara’a ya zarce gonar,
Auduga ni na yi shaida.

Mun gaisa har da Sale,
Aboki gun Bukar ne,
Dattijo ne na gaske,
Mai barkwanci da ilmi,

Ya koyi halin Aminu,
Ya min saukar mutumci,
Baƙo daraja gare shi,
Wajen Manzo na Hafsa.

Garin Biu in da hali,
Can zan koma na tare,
Na yi noma har da rani,
Arziki na nan a noma.

Ba shakka da da dama,
Garin Biu za na koma,
Don nai kiwon awaki,
Shanu kaji tumaki.

Garin Biu na da Dokta
Wani mai kishin ƙasarmu,
Mota kayan jikinsa,
Da gida tutar ƙasa ne.

Komai ka gani gare,
Kalar tutar ƙasa ne,
Har takalmin ƙafarsa,
Hula tutar ƙasa ne.

Garin Biu jami’a ce,
Akwai darussa na ɗauka,
Tafkin Tila in ka ɓulla,
Ka sha kallo ka more,

Abin ajabi a tafkin,
Yana da yawa na dubi,
Kadoji na ta kiwo,
Kifaye na ta yawo.

Akwai lantarki na aiki.
Cikin Biu kulliyaumin,
Makarantu jami’o’i,
Akwai da yawa ƙasar Biu.

Jami’ar sojan ƙasarmu,
Garin Biu ne masauki,
Ƙasar Biu na da faɗi,
Masarauta ce daɗaɗɗa.

Mutan Biu na da kishi,
Sun raya garinsu sosai,
Ni na ga hakan da kaina,
Lokuna lungu da saƙo.

Dukkan titi da sola,
Ko’ina haske ka duba,
Titunan Biu babu rami,
Shugabanni na da kishi.

‘Yan siyasa masu aiki,
Su ke zaɓa wa kansu,
Ba sa zaɓe makance,
Sai sun tace su darje.

Dukkan titin garin Biu
Da kwata ta ruwa a gefe,
Wakilinsu da ke Abuja,
Shi Betara ɗan halak ne.

Wanda ke kishin garinsu,
Jinjina tilas gare shi,
Da a ce da irinsu dozin,
An bar kuka Arewa.

‘Yan ƙasar Biu jarumai,
Burutai babban Janar,
Fanni-fannin ƙwararru,
‘Ya’yan Biu za a gan su.

A nan zan jefa aya,
Khalid na je ziyara,
Imam na je da kaina,
Ƙasar Biu nai zumunci.

__________

(HM) Khalid Imam
A Garin Biu
7:33ND
11 ga wata Afirelu, 2024

Previous Post

Ruhin Bukar Usman

Next Post

SARAUTA TUSSLE: The Debacle in Kano State

Related Posts

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza
Adabi

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

April 11, 2026
FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)
Adabi

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

March 7, 2026
Let’s Speak Our Mother Tongue
Adabi

Mu Yi Kishi Da Alfahari Da Harshen Uwa

March 6, 2026
Next Post
SARAUTA TUSSLE: The Debacle in Kano State

SARAUTA TUSSLE: The Debacle in Kano State

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

RAMADAN KARIM: 10-1447

RAMADAN KARIM: 10-1447

February 27, 2026
KAMUN LUDAYIN JEMAGE

KAMUN LADUYIN JEMAGE (19-08-2023)

August 20, 2023
Lt. Col. Danjuma’s Book: Captivating Insight Into Civil-Military Relations In Nigeria

Lt. Col. Danjuma’s Book: Captivating Insight Into Civil-Military Relations In Nigeria

January 22, 2024
Lallai Hukuma Ta Tallafa Wa Marubuta Domin Yaƙar Jahilci – Sheikh Gamawa

Lallai Hukuma Ta Tallafa Wa Marubuta Domin Yaƙar Jahilci – Sheikh Gamawa

July 18, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa
  • Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye
  • Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

April 16, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.