• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, January 16, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Adabi

HAWAYE DON AFIRKA

Dr. Hadiza Nuhu, OON by Dr. Hadiza Nuhu, OON
August 16, 2023
in Adabi
0
HAWAYE DON AFIRKA
50
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

HAWAYE DON AFIRKA

Daga Dokta Hadiza Nuhu, OON

Related posts

SAKAMAKON ZAGAYE NA BIYU NA GASAR RUBUTU TA GIDAUNIYAR ZANNA-WALI (2025)

SAKAMAKON ZAGAYE NA BIYU NA GASAR RUBUTU TA GIDAUNIYAR ZANNA-WALI (2025)

December 23, 2025
Dalilan Da Suka Sanya Na Rubuta Littafin Tarihin Maitatsine

Dalilan Da Suka Sanya Na Rubuta Littafin Tarihin Maitatsine

December 6, 2025

~~~~~~~
A yayin da ake ta laluben hanyoyin samun maslaha tsakanin Ƙungiyar ECOWAS da Sojojin da suka hamɓarar da Gwamnatin Farar Hula a Jamhuriyyar Nijar, ita kuwa Dokta Hadiza Nuhu, OON alƙalami ta ɗauka ta zubar da hawayen takaici domin ceto Arewa da Niger da Nigeria da ma  Afirka gaba ɗaya

Dr. Hadiza Nuhu, OON

daga makircin ‘yan duniya da ke son jefa al’ummarta cikin uƙubar yaƙi. Ga baitukan, kamar yadda ta rero su:
~~~~~~~

Bismillah Rabbi Sarki Tabaraka,
Ga ni ɗauke da baituka,
Ba ni hikima da ɗaukaka,
Zan zo da zance na ECOWAS.

Na yi salati ga Hamidu,
Muhammadu Manzo Mujaddadu,
Shi ya yi yaƙi da hakidu,
A cikin aiki na ECOWAS.

Jama’a ku ba ni kunnuwa,
Ga Nijar ana kururuwa,
An tsananta dukkan abubuwa,
A yunƙurinsu na ECOWAS.

Ga sojoji da bindiga,
Sun sheƙo za su daddaga,
Ta Nijar sun ka ɓuɓɓuga,
Niyyarsu AREWA ECOWAS.

Mun gane wayon da jijjifi,
Arewa a take da yayyafi,
Da ruwan bala’in ƙarfi.
Mun gane hila ta ECOWAS.

Tarenmu ce za a wargaza,
An fake don rugurguza,
An kitso girin ragargaza,
Sai anka ɓullo ta ECOWAS.

Sabonsu kullum su ɓarnata,
Kuka ake babu kurumta,
Duniya duk an maganta,
Su ba ruwansu ECOWAS.

Shin ita ba ƙungiya ce ba?
Ta haɗin kan ƙasar baba?
Jimilla sha biyar duba?
Ƙasashenta ita ECOWAS?

Ita ba mai tallafi ce ba?
Don ci gaban ƙasashen ba?
Ba ta cin zarafi ce ba?
Shin ina manufarta ECOWAS?

Ya za ta juye da yaudara?
Za tai yaƙi cikin gadara?
Da ‘yan gidanta tsirara?
Ko wannan shi ne ECOWAS?

Shin ko ‘yar kanzagi ce?
Ta tsofaffin fatake ce?
Sanannun masu ƙwace?
Kar fa a yaudare ki ECOWAS!

Su fa ‘yan duniya jari ne.
Aikinsu zamba yaudara ne,
‘Yan mallaka da ƙwace ne.
Gara ki farka fa ECOWAS.

Aikinsu su dai su bautar,
Dukiya sun ka ƙwatar,
Ƙasashenmu sun durƙusar,
Lallai ki guje su ECOWAS.

Sun kashe ‘yan kishin ƙasa,
Masoyanmu a cikin ƙasa,
Janar Murtala mai ƙasa.
To a hir ɗin ki ECOWAS.

Mu’ammar Gaddafi jarumi,
Thomas Sankara hakimi,
Mun rasa su sai jimami,
Ko kin manta ne ECOWAS.

Su ne dillalan makamai,
Masu rarraba mukamai,
Sun haddasa yaƙi maimai,
Ba za mu amince ba ECOWAS.

Ga su nan suna ta leƙe,
Sun biyo mu a hayyaƙe,
Mu bar waige ido mu feƙe,
Mu san sirrinsu ECOWAS.

Akwai ‘yan kanzagin cikinmu,
Shugabanni ruɓabbun wajenmu,
Kwaɗayinsu sui ta mulkinmu,
Ba kishin ƙasa ba ECOWAS.

Ba ruwansu da talakka,
Suna tai masa takakka,
Talauci yunwa makaka,
Ki buɗe idonki ECOWAS.

Babu tsaro a cikin ƙasa,
Sun hana illimin matasa,
Ba aiki sana’a ‘yan ƙasa,
Ya kaiconmu kin ji ECOWAS.

Wallahi duk gwanin tausayi,
Jama’a mu yo tsinkayi,
Salon bauta cikin laulayi,
Habawa ke ko ECOWAS!

Kai waɗannan shugabanni,
Ko mu kira su “wau-gabanni”
Burinsu su sa mu cikin bani.
Ina kike ne yanzu ECOWAS?

Sun kira kuraye daga sassa,
Ga Babbar Fara Farar Saa
Mabiyarta Marka tasa,
Kin san da zamansu ECOWAS.

Ga algunguma ita Guila,
Za tai mana kisan gilla,
Sun haɗa kai sun ƙulla,
Sun shigo su ta ECOWAS.

Fafiratan ba mu yarda ba.
Nijar da mu gida babba
Tun Marka ma ba ta zo ba,
Gidan duniya bare ECOWAS.

Mujaddadi can ya faru,
Aikinsa sai ka ji ƙaru,
‘Yan mallaka sun ka taru,
Sun ka raba mu ECOWAS.

Sunka haɗa mu da bare,
Su masu ɗaukar taɓare
Zage-zage halinsu zare,
Zo ki gane ke ECOWAS.

‘Yan Nijar akwai halacci,
Ba su batu na ƙasƙanci,
Babu ruwansu yin butulci,
Suna son mu kin ji ECOWAS.

Su ‘yan uwa ne a Musulunci,
Shacin iyaka bai halacci,
Iyakar ta mallakar ƙunci,
Ba mai raba mu ECOWAS.

Ku ‘yan Arewa ga gargaɗi,
Ɓatan ɓaƙatantan ba daɗi,
Ku rasa Kuɗun can tabɗi!
Ku rasa Nijar ga ECOWAS.

Allah ni dai na yi roƙo,
Dunƙule mu kamar ƙoƙo,
Nijar da Arewa ƙara maiƙo,
Na zumunci ko babu ECOWAS.

Mu huce zagin Biyafarawa,
‘Yan Oduduwa ma sun taɓawa,
Mu ne abin ƙi Najeriyar Arewa,
Ga shi an zo da ECOWAS.

Kar mu sake mui butulci,
Nasara nufinsa ya yi ɓaci,
Ya shata layi don rabon ci,
Kar ki biya shi kin ji ECOWAS.

Duniya ta gan mu ɗinke,
Kar mu rabe don su banke,
Ɗaidaikunmu za su make,
Sannan su hada da ECOWAS.

Haba Tinubu mun ji haushi,
Kalamanka sun yi kaushi,
A kan Nijar har ka tashi,
Razana mu da ECOWAS.

Lallai ka sani shi zalunci,
Bai sa mulki yai inganci,
Tafi sannu kar kai ƙaskanci,
Kar ka biye wa ita ECOWAS.

Fara Fararsa da ita Marka,
Haɗa da Guila sai ka farka
Cin amana su sunka tafka.
Najeriyarka ta fi ECOWAS.

Najeriyarmu duk mun san ta,
Matsaloli duk sun cika ta
Nemo maganinsu don ta huta,
Ka ƙyale batun wofi na ECOWAS.

Yunwa fatara babu tsaro,
Watanka biyu duk ka faro,
Mulkinka yau mun ji tsoro,
Kana ta batu na ECOWAS.

Arewa dai tai maka gata,
Ta yi halacci babu rata,
Ta zabe ka jiya da gata,
Babu hannun ita ECOWAS.

Kai za ka kare dimokuraɗiyya?
Ka ƙyale Nijar ‘yantacciya
Ka dawo ta mu Jamhuriyya
Ka gyara ƙyale ECOWAS.

Ka sani yaƙi shi haɗari ne,
Arewa ba ta son yaki ne,
Da Nijar tun da ‘yan uwa ne,
Kar ka biye zugar ta ECOWAS.

Ni Khadijah na yi nawa,
Sai ku ƙara fahimtarwa,
Allah ka yi mana afuwa
Raba mu da makircin ECOWAS.

Haɗa kanmu duka cikin aminci,
Allah daɗo rahamarKa mai ci,
Ka wadata mu da abinci,
Ka warware tuggunta ECOWAS!
~~~~~~~

Previous Post

Janar Faruk Yahaya Ya Zama Zaruman Sakkwato

Next Post

Huɗubar Jumu’a A Taƙaice Daga Masallacin Unguwar Tumbu-Madallah

Related Posts

SAKAMAKON ZAGAYE NA BIYU NA GASAR RUBUTU TA GIDAUNIYAR ZANNA-WALI (2025)
Adabi

SAKAMAKON ZAGAYE NA BIYU NA GASAR RUBUTU TA GIDAUNIYAR ZANNA-WALI (2025)

December 23, 2025
Dalilan Da Suka Sanya Na Rubuta Littafin Tarihin Maitatsine
Adabi

Dalilan Da Suka Sanya Na Rubuta Littafin Tarihin Maitatsine

December 6, 2025
Yau Take Juma’a: Allah Ka Albarkace Mu
Adabi

Yau Take Juma’a: Allah Ka Albarkace Mu

December 5, 2025
Next Post
Huɗubar Jumu’a A Taƙaice Daga Masallacin Unguwar Tumbu-Madallah

Huɗubar Jumu'a A Taƙaice Daga Masallacin Unguwar Tumbu-Madallah

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Abdulkadir Nasir is the New CoS to Katsina State Governor

Abdulkadir Nasir is the New CoS to Katsina State Governor

December 12, 2024
2027 and the Rise of a Third Force: Can ADC’s Political Heavyweights Unseat Tinubu?

SHIN KO GAMAYYAR ‘YAN ADAWA NA JAM’IYYAR ADC ZA SU IYA KADA TINUBU A 2027?

July 3, 2025
Tunawa Da Umar Sa’idu Tudunwada

Tunawa Da Umar Sa’idu Tudunwada

July 1, 2023
Buthelezi Ɗan Kishin Ƙasa Ya yi Bankwana Da Duniya

Buthelezi Ɗan Kishin Ƙasa Ya yi Bankwana Da Duniya

September 10, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation
  • Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco
  • Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

January 15, 2026
Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

January 14, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.