Daga Muhammad Aminu Kabir
An rantsar da Majalisa ta Goma ban da Amadu. Wannan abu bai mani daɗi ba. Na san kuma mutane da daman gaske da suka riƙa kira na suna mani jaje bisa wannan rashin da muka yi, kodayake ba ni yankin da Sanata ya fito amma alheransa sun riski mutane da dama da ba su fito daga yankin nasa ba. Wannan ne ma dalilin da ya sa suka yi kukan rashin sa, ba ma iya Jihar Katsina ba har da maƙwabtanta. Allah Ya sauya maka da alheri, Amadu.
Allah Sarki! A ko’ina ka ambaci sunan Sanata Ahmad Babba Kaita, ba wai Jihar Katsina ba duk faɗin ƙasar nan, za ka ji ana yabon shi, ana rububin samun shi. Ba don komai ba, ba sai don saboda ƙoƙarinsa wajen ganin ya samar da ayyukan alheri ga al’umma ba ma ga waɗanda yake wakilta a zauren Majalisar Ƙasa ba, a’a a kaf faɗin Jihar Katsina da ma Najeriya baki ɗaya.
Sanata Kaita ya kasance mutum mai tausayi mai kuma son taimakon jama’a. A kodayaushe burinsa ya taimaka wa al’umma da gwargwadon abin da Allah Ya hore masa.
Hausawa suka ce yabon gwani ya zama dole, sannan sakamakon alheri shi ne alheri! Muna addu’ar ayyukan alherin da wannan bawan Allah ya yi, Allah Ya yi masa kyakkyawan tanaji da su a nan duniya da kuma gobe ƙiyama.
Kowane ɗan Adam tara yake bai cika goma ba, kamar yadda Hausawa suke cewa. Ina addu’a, Allah Ya yafe wa Amadu kurakuran da ya yi a lokacin gudanar da jagorancinsa.
Nasara ko faɗuwa zaɓe dukkaninsu idan aka yi nazari, alheri ne. Na farko, yana sanya ka farin ciki, domin ka yi nasara. Allah kuma Ya ɗora maka wani nauyi na gudanar da ayyukan al’umma, wanda sai dole ka nemi taimakon Allah da al’umma su taya ka wajen sauke nauyin da Allah Ya ɗora maka.
Yayin da na biyun kuma wato faɗuwa zaɓe, za ta sanya ka ka koma baya ka yi nazarin a ina ka samu matsala ko ka yi kurakurai domin ka gyara.
Ina addu’ar Allah Ya ba ka ikon yin tunani mai kyau tare da samar da gyara a inda kake da kurakurai, Malam Amadu.
A kullum idan ina nazari a kan lamarin Amadu, abu na farko da yake faɗo mani a rai shi ne, me ya sa wasu daga cikin mutanen Kankiya suke faɗa da shi, ciki kuma har da waɗanda ya taimaka ma su? Wasu da na ji ta bakinsu ƙalilan, suna cewa ta yaya za a bai wa wasu aiki ba a ba su ba, su da suke yankin da Amadu yake? Irin waɗannan da sauran ƙorafe-ƙorafe, mafi yawa idan ka saurare su, za ka ji ƙorafin na ƙashin kaine ba na al’umma ba. Amma ba su alfahari da cewa ɗansu ya yi wa wasu alheri, har duniya tana yabon shi?
Ni dai alhamdu lillah! Ban da wakilci da Amadu yake tare da gudanar da ayyukan samar da ci gaban ƙasa da yake ƙoƙarin samarwa ta hanyar ofis ɗinsa ga lunguna da saƙon Jihar Katsina, zan tuna da Amadu a kodayaushe da yadda yake taimakon marasa ƙarfi wajen samar da lafiya ko neman lafiya, Amadu ya tallafi iyalai da daman gaske, waɗanda tun ina lissafi har ya ƙwace mani, ba ta hanyata kaɗai ba, ta hanyoyi daban-daban. Allah Ya saka da alheri. Amin.
Ina maka addu’ar fatan alheri tare da neman gafarar Allah yafiya a kan kurakuranka, Malam Amadu
Wassalamu Alaikum yallaɓai!













