• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, January 16, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Siyasa

Sanata Ahmad Babba Kaita: Ba Rabo Da Gwani Ba

Jihar Katsina Ta Yi Rashin Gwarzo A Majalisa

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
June 14, 2023
in Siyasa
0
Sanata Ahmad Babba Kaita: Ba Rabo Da Gwani Ba

Ahmad Kadaura

74
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Daga Muhammad Aminu Kabir

An rantsar da Majalisa ta Goma ban da Amadu. Wannan abu bai mani daɗi ba. Na san kuma mutane da daman gaske da suka riƙa kira na suna mani jaje bisa wannan rashin da muka yi, kodayake ba ni yankin da Sanata ya fito amma alheransa sun riski mutane da dama da ba su fito daga yankin nasa ba. Wannan ne ma dalilin da ya sa suka yi kukan rashin sa, ba ma iya Jihar Katsina ba har da maƙwabtanta. Allah Ya sauya maka da alheri,  Amadu.

Related posts

Komawar Kwankwaso Zuwa APC: Gaba Kura Baya Sayaki

Abubuwan Da Za Su Iya Faruwa Idan Kwankwaso Ya Koma APC

September 28, 2025
KWANKWASO BAI CIKIN WAƊANDA SUKA KAFA APC

KWANKWASO BAI CIKIN WAƊANDA SUKA KAFA APC

September 22, 2025

Allah Sarki! A ko’ina ka ambaci sunan Sanata Ahmad Babba Kaita, ba wai Jihar Katsina ba duk faɗin ƙasar nan, za ka ji ana yabon shi, ana rububin samun shi. Ba don komai ba, ba sai don saboda ƙoƙarinsa wajen ganin ya samar da ayyukan alheri ga al’umma ba ma ga waɗanda yake wakilta a zauren Majalisar Ƙasa ba, a’a a kaf faɗin Jihar Katsina da ma Najeriya baki ɗaya.

Sanata Kaita ya kasance mutum mai tausayi mai kuma son taimakon jama’a. A kodayaushe burinsa ya taimaka wa al’umma da gwargwadon abin da Allah Ya hore masa.

Hausawa suka ce yabon gwani ya zama dole, sannan sakamakon alheri shi ne alheri! Muna addu’ar ayyukan alherin da wannan bawan Allah ya yi, Allah Ya yi masa kyakkyawan tanaji da su a nan duniya da kuma gobe ƙiyama.

Kowane ɗan Adam tara yake bai cika goma ba, kamar yadda Hausawa suke cewa. Ina addu’a, Allah Ya yafe wa Amadu kurakuran da ya yi a lokacin gudanar da jagorancinsa.

Nasara ko faɗuwa zaɓe dukkaninsu idan aka yi nazari, alheri ne. Na farko, yana sanya ka farin ciki, domin ka yi nasara. Allah kuma Ya ɗora maka wani nauyi na gudanar da ayyukan al’umma, wanda sai dole ka nemi taimakon Allah da al’umma su taya ka wajen sauke nauyin da Allah Ya ɗora maka.

Yayin da na biyun kuma wato faɗuwa zaɓe, za ta sanya ka ka koma baya ka yi nazarin a ina ka samu matsala ko ka yi kurakurai domin ka gyara.

Ina addu’ar Allah Ya ba ka ikon yin tunani mai kyau tare da samar da gyara a inda kake da kurakurai, Malam Amadu.

A kullum idan ina nazari a kan lamarin Amadu, abu na farko da yake faɗo mani a rai shi ne, me ya sa wasu daga cikin mutanen Kankiya suke faɗa da shi, ciki kuma har da waɗanda ya taimaka ma su? Wasu da na ji ta bakinsu ƙalilan, suna cewa ta yaya za a bai wa wasu aiki ba a ba su ba, su da suke yankin da Amadu yake? Irin waɗannan da sauran ƙorafe-ƙorafe, mafi yawa idan ka saurare su, za ka ji ƙorafin na ƙashin kaine ba na al’umma ba. Amma ba su alfahari da cewa ɗansu ya yi wa wasu alheri, har duniya tana yabon shi?

Ni dai alhamdu lillah! Ban da wakilci da Amadu yake tare da gudanar da ayyukan samar da ci gaban ƙasa da yake ƙoƙarin samarwa ta hanyar ofis ɗinsa ga lunguna da saƙon Jihar Katsina, zan tuna da Amadu a kodayaushe da yadda yake taimakon marasa ƙarfi wajen samar da lafiya ko neman lafiya, Amadu ya tallafi iyalai da daman gaske, waɗanda tun ina lissafi har ya ƙwace mani, ba ta hanyata kaɗai ba, ta hanyoyi daban-daban. Allah Ya saka da alheri. Amin.

Ina maka addu’ar fatan alheri tare da neman gafarar Allah yafiya a kan kurakuranka, Malam Amadu

Wassalamu Alaikum yallaɓai!

Previous Post

Shauƙin Son Faɗakarwa Ya Sa Na Zama Mawaƙi – ABDUL EXTRA

Next Post

Shekara 10 Baya: Tunawa Da Malam Suleiman Muhammad

Related Posts

Komawar Kwankwaso Zuwa APC: Gaba Kura Baya Sayaki
Siyasa

Abubuwan Da Za Su Iya Faruwa Idan Kwankwaso Ya Koma APC

September 28, 2025
KWANKWASO BAI CIKIN WAƊANDA SUKA KAFA APC
Siyasa

KWANKWASO BAI CIKIN WAƊANDA SUKA KAFA APC

September 22, 2025
JONATHAN – KWANKWASO: Sabon Lissafin 2027
Siyasa

JONATHAN – KWANKWASO: Sabon Lissafin 2027

August 15, 2025
Next Post
Shekara 10 Baya: Tunawa Da Malam Suleiman Muhammad

Shekara 10 Baya: Tunawa Da Malam Suleiman Muhammad

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Mutane Sun Koma Tafiya Ƙasa A Abuja

Mutane Sun Koma Tafiya Ƙasa A Abuja

July 20, 2023
Daura Gidan Tarihin Hausa

Daura Gidan Tarihin Hausa

October 30, 2025
HARIN JIRGIN SAMA GA MUSULMI: Ya Wajaba A Zurfafa Bincike Kuma A Biya Diyya

HARIN JIRGIN SAMA GA MUSULMI: Ya Wajaba A Zurfafa Bincike Kuma A Biya Diyya

December 7, 2023
Taya Murna Ga Injiniya Muntari Sagir

Taya Murna Ga Injiniya Muntari Sagir

October 24, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation
  • Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco
  • Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

January 15, 2026
Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

January 14, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.