Da Alama Super Eagles Za Su Kawo Kofin AFCON Bana
~~~~~~~
✓A jiya dai Allah Ya ba Najeriya sa’a, ta doke Kwaddabuwa a gidanta. Wannan babbar alama ce ta nasara.
✓Idan za mu waiga baya a shekarar 1994, Super Eagles sun doke Kwaddabuwa kuma Allah da ikonSa suka cinye Kofin AFCON a shekarar.
✓Haka ma a shekarar 2013, Najeriya ta doke Kwaddabuwa kuma ta cinye Kofin AFCON.

✓To kuma ga shi bana ma, 2024, an sake kwatawa, Super Eagles sun yi wa Kwaddabuwa 1-0. Akwai alamar in sha Allahu za su ɗauko kofin.
~~~~~~~
JAMA’A YAYA KUKE GANI KUMA WANE FATA ZA KU YI WA SUPER EAGLES?
~~~~~~~













