• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Sunday, May 24, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Labarai

Ƙasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Yi Tir Da Hare-Haren Sojojin Isra’ila A Zirin Gaza

Daga Wakilinmu by Daga Wakilinmu
November 15, 2023
in Labarai
0
Ƙasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Yi Tir Da Hare-Haren Sojojin Isra’ila A Zirin Gaza

Shugaba Tinubu tare da Yariman Saudiyya

14
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Ƙasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Yi Tir Da Hare-Haren Sojojin Isra’ila A Zirin Gaza

Taron Haɗin Guiwar Ƙasashen Larabawa da sauran ƙasashen Musulmai, ya yi tir tare da nuna rashin amincewa kan hare-haren da sojojin Isra’ila ke ci gaba da kaiwa a Gaza.

Related posts

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026

Taron wanda aka gudanar ranar Asabar, 11 ga Nuwamba, ya bayyana cewa abin da sojojin Isra’ila suka yi laifin tsallake ƙa’idoji da sharuɗɗan yaƙi ne, kuma dabbanci ne kan Falasɗinawa fararen hula.

Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris ne ya tabbatar da haka, a cikin wata sanarwar da Jami’in Yaɗa Labarai na ministan, Rabi’u Ibrahim ya fitar.

Idris, wanda ya na cikin tawagar Shugaban Ƙasa Bola Tinubu a wurin taron, ya ƙara da cewa kuma an yi kira da a gaggauta gudanar da gagarimin taron duniya, inda za a bijiro da hanyoyin tabbatar da wanzuwar zaman lafiya a yankin Falasɗinu.

Sanarwar bayan taron da wanda shugabannin ƙasashen Ƙungiyar OIC da na Majalisar Ƙasashen Larabawa suka halarta, an yi kira da a gaggauta tsagaita dukkan hare-haren da sojojin Isra’ila ke kaiwa a yankin Gaza.

Kuma sun fito ƙarara sun ce farmakin da Isra’ila ke kaiwa kan Gaza ci gaba ne da irin mamayar da ta yi wa Falasɗinawa a 1967 a yankin Gaza, West Bank, Al-Quds Al-Sharif da kuma Arewacin Jerusalem.

Sannan kuma taron ya buƙaci Majalisar Ɗinkin Duniya ta fito da ƙwaƙƙwarar matsaya a ƙarƙashin Majalisar Tsaro ta Majalisar Ɗinkin, wadda za ta tilasta daina duk wani nau’i da salo na gallazawa da Isra’ila ke yi wa Falasɗinawa.

Haka nan kuma wannan taro ya nemi Isra’ila ta kawo ƙarshen mamayar da ta ke yi a yankin, domin ya karya ƙa’ida da iyakokin da dokokin ƙasa da ƙasa suka shar’anta.

Sun ce musamman farmakin ya saɓa wa ƙa’idar Majalisar Ɗinkin Duniya mai lamba AES-101.25, ta ranar 26 ga Oktoba, 2013.

A wurin taron, shugabannin sun yi kakkausan kira ga Majalisar Tsaro ta Majalisar Ɗinkin Duniya cewa “ta gaggauta yin Allah-wadai da dabbacin da sojojin Isra’ila ke kan yi na ruguza asibitoci a Zirin Gaza. Kuma ta yi tir kan hana a shigar wa Falasɗinawa da magunguna, abinci fetur da katse wutar lantarkin da mahukuntan Isra’ila ɗin suka yi a Zirin Gaza.”

An zartas da cewa matuƙar Majalisar Ɗinkin Duniya ta ƙi yin tir da dabbancin da sojojin Isra’ila ke aikatawa a Zirin Gaza, to tamkar ta halasta mummunan kisan da ake wa fararen hula ne da suka ƙunshi ƙananan yara, dattawa, mata da kuma ruguza Gaza da ake kan yi.

Sun ce ya zama wajibi Isra’ila ta ɗage takunkumin datse Zirin Gaza da ta yi, tsawon shekaru masu yawa.

Sannan kuma taron ya yi tir dangane da yadda wasu ƙasashe suka riƙa taimaka wa Isra’ila da muggan makaman da take amfani da su, ta na kisan gilla kan Falasɗinawa, tare da ruguza masu gidaje, asibitoci, makarantu, masallatai, coci-coci da sauran wuraren more rayuwa.

Previous Post

INEC Ta Nesanta Kanta Daga Zargin Baddala Ƙuri’un Zaɓen Gwamnan Kogi

Next Post

SAI AN YI DA GASKE: Littafin Wasan Kwaikwayo A Mizanin Nazari Da Sharhi

Related Posts

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi
Labarai

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Labarai

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina
Labarai

Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina

February 13, 2026
Next Post
SAI AN YI DA GASKE: Littafin Wasan Kwaikwayo A Mizanin Nazari Da Sharhi

SAI AN YI DA GASKE: Littafin Wasan Kwaikwayo A Mizanin Nazari Da Sharhi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Burina Rubutuna Ya Zama Silar Shiriyar Al’umma – Antin Kaduna

Burina Rubutuna Ya Zama Silar Shiriyar Al’umma – Antin Kaduna

September 10, 2023
Kwankwaso’s Return to APC: Between the Devil and the Deep Blue Sea

Kwankwaso’s Return to APC: Between the Devil and the Deep Blue Sea

July 11, 2025

June 27, 2025
TSOKACINMU NA YAU (21)

TSOKACINMU NA YAU (21)

March 21, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • POSITIVE COMRADE
  • BUKAR USMAN: The Human Library
  • Sule Lamido’s Theme of Authenticity

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

POSITIVE COMRADE

POSITIVE COMRADE

May 20, 2026
BUKAR USMAN: The Human Library

BUKAR USMAN: The Human Library

May 19, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.