BABANA
~~~~~~~
A ranar Litinin 31-10-2005 (Miladiyya),
Wacce ta yi daidai da 28 ga Ramadan, 1426 (Hijiriyya),
Allah Ya amshi ran mahaifina, Malam Yahuza.
MUNA ROƘON ADDU’A DAGA GARE KU!
~~~~~~~
Wannan shi ne mahaifina,
Ya rayu can wata rana.
Shi ne tsoka a ruhina,
Jininsa ke tafiya a raina.
Shi ne ZAKARA a gidana,
Bai yo gadarar neman suna.
Shi ya riƙe ƙaunar mamana,
Sun shayar da ni ƙauna.
Ya ganar da ni kaina,
ILIMI shi ne mutuncina.
Ya yo kimtsi ga ɓargona,
Don in riƙon ’yan uwana.
Ya yo zumunci duk rana,
Ba ya wulaƙanci ko raina.
Burinsa kowa ya yi rana,
Ba ya baƙin rai mai ƙuna.
Yau kam babu shi BABANA,
Ya koma wurin MAHALICCINA.
ALLAH muke roƙo Ya tuna
Shi Ya ba shi ALJANNA!
Amin Allah ƙaro mana,
Fatahin tallafar mahaifana!
~~~~~~~
© Bashir Yahuza Malumfashi
Litinin 04-04-1444 (Hijiriyya)
31-10-2022 (Miladiyya)
~~~~~~~













