• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Monday, August 24, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Addini

Huɗubar Jumu’a Daga Limamin Masallacin Tumbu-Madallah

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
July 28, 2023
in Addini
0
Huɗubar Jumu’a Daga Limamin Masallacin Tumbu-Madallah

Limamin Masallacin Tumbu-Madallah

34
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Huɗubar Jumu’a Daga Limamin Masallacin Tumbu-Madalla

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Extremism, Laxity and Moderation in Islam

Musulunci Ba Addinin Tsauri Ko Sakaci Ba Ne…

August 21, 2026
Al’amuran Tsaro: Musulmin Duniya Sun Taru A Abuja

Al’amuran Tsaro: Musulmin Duniya Sun Taru A Abuja

August 12, 2026

A yau Juma’a, 10-01-1445 (Hijriyya) = 28-07-2023, Limamin Masallacin Unguwar Tumbu da ke garin Madalla, Ƙaramar Hukumar Tafa, Jihar Neja, ya gabatar da huɗuba, wacce maudu’inta ya kasance “Muhimmancin Sallar Juma’a A Musulunci.”

Bayan gabatarwa, girmamawa da yabo ga Allah (swt) da sallama da salati ga fiyayyen talikai, Manzon Allah, Muhammadu (saw), Liman ya jawo hankalin al’umma da mu ji tsoron Allah, mu riƙe Musulunci da gaske. Ya ce mu sani fa Allah Ya cika mana addininmu, wanda shi ne babbar ni’imar da babu kamar ta a bayan ƙasa.

Ya bayyana mana cewa Allah Ya farlanta mana rukunonin addini guda biyar, ciki kuwa har da salloli biyar a rana, ciki kuwa har da Sallar Juma’a.

Kamar yadda Liman ya nusar da mu, yana daga falalar Sallar Juma’a mutum ya yi gaggawar zuwa masallaci, domin samun babban rabo. Kada mutum ya sake wani abu ya shagaltar da shi daga halartar Sallar Juma’a.

Liman ya nusar da mu wasu daga ladubban Jumu’a – mutum ya yi wanka, ya yi alwala, ya saka sutura mai kyau da turare mai ƙanshi. Mutum ya yi nafilfili, ya yi salati mai yawa ga Manzon Allah (saw). Mutum ya natsu ya saurari huduba, kada ya yi magana da kowa.

Liman ya sanar da mu wani hadisi na Manzon Allah, wanda ke cewa babu Jumu’a ga duk wanda ya yi magana a yayin huɗubar Jumu’a.

Haka kuma ya sake kwaɗaitar da al’umma game da falalar Sallar Juma’a, inda ya sanar da mu wani hadisi, inda Manzon Allah (saw) ke cewa, duk wanda ya yi alwala, ya je Sallar Juma’a, ya yi nafila, ya samu huɗuba, to an yafe masa zunubbansa na makon, har ma da ƙarin kwana uku gaba.

Liman ya tsoratar da mu ga barin Sallar Juma’a. Ya kafa mana shaida da hadisin Manzon Allah (saw), cewa duk wanda ya yi fashin Sallar Jumu’a sau uku a jere, ba tare da wani uzuri amsasshe ga Shari’a ba, to an rufe zuciyarsa.

Wanda kuwa ya bari Allah Ya rufe masa zuciya, tabbas ya taɓe. Allah Ya kiyashe mu, Amin.

Malam Ya ja hankalinmu da mu guji yin duk wata hulɗa ta kasuwanci ko aiki a daidai lokacin Sallar Jumu’a, domin kuwa haramun ne. Amma babu laifi mutum ya koma bakin aikinsa ko sana’a, da zarar an kammala Sallar Jumu’a.

Malam ya rufe huɗubarsa da kyakkyawar addu’a ga al’ummar ƙasa. Allah Ya sa mu dace da rahamarSa, Ya ba mu lafiya da zaman lafiya da imani da yalwar arziki. Amin.

Previous Post

Yau Ne Maulidin Likitar Ma’aurata

Next Post

An Samar Da Maslaha A Takaddamar Sheikh Idris Da Gwamnatin Bauchi

Related Posts

Extremism, Laxity and Moderation in Islam
Addini

Musulunci Ba Addinin Tsauri Ko Sakaci Ba Ne…

August 21, 2026
Al’amuran Tsaro: Musulmin Duniya Sun Taru A Abuja
Addini

Al’amuran Tsaro: Musulmin Duniya Sun Taru A Abuja

August 12, 2026
BARKA DA SABUWAR SHEKARAR MUSULUNCI 1448 HIJIRIYYA
Addini

BARKA DA SABUWAR SHEKARAR MUSULUNCI 1448 HIJIRIYYA

June 16, 2026
Next Post
An Samar Da Maslaha A Takaddamar Sheikh Idris Da Gwamnatin Bauchi

An Samar Da Maslaha A Takaddamar Sheikh Idris Da Gwamnatin Bauchi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Yau Za A Fafata Tsakanin Canada Da Bosnia-Herzegovina

Yau Za A Fafata Tsakanin Canada Da Bosnia-Herzegovina

June 12, 2026
YADDA NA ƊAUKI SHEIKH YAKUBU YAHAYA KATSINA

YADDA NA ƊAUKI SHEIKH YAKUBU YAHAYA KATSINA

July 19, 2025
SHUGABA BUHARI: TA’AZIYYAR JAN GWARZO

SHUGABA BUHARI: TA’AZIYYAR JAN GWARZO

July 20, 2025
WILL ATIKU’S EXIT FROM THE PDP BRING HIM VICTORY IN 2027?

WILL ATIKU’S EXIT FROM THE PDP BRING HIM VICTORY IN 2027?

July 19, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Professor Bello Sa’idu: The Demise of Literary Icon
  • Bankwana Da Jigon Adabi: Ta’aziyyar Farfesa Bello Sa’idu
  • Musulunci Ba Addinin Tsauri Ko Sakaci Ba Ne…

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Bankwana Da Jigon Adabi: Ta’aziyyar Farfesa Bello Sa’idu

Professor Bello Sa’idu: The Demise of Literary Icon

August 23, 2026
Bankwana Da Jigon Adabi: Ta’aziyyar Farfesa Bello Sa’idu

Bankwana Da Jigon Adabi: Ta’aziyyar Farfesa Bello Sa’idu

August 22, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.