• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Monday, August 24, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

TALAUCI: Yadda Matasan Arewa Ke Gararamba A Legas A Wulaƙance

Abbas Ibrahim Ɗalibi by Abbas Ibrahim Ɗalibi
October 4, 2023
in Babban Labari
0
TALAUCI: Yadda Matasan Arewa Ke Gararamba A Legas A Wulaƙance
23
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

TALAUCI: Yadda Matasan Arewa Ke Gararamba A Legas A Wulaƙance

Daga Abbas Ibrahim Ɗalibi

Related posts

Ɗalibin Jami’ar Sojoji Ya Ƙera Robot Mai Kashe Gobara

Ɗalibin Jami’ar Sojoji Ya Ƙera Robot Mai Kashe Gobara

August 12, 2026
Rarara Ya Ƙara Haska Farin Jinin Sheikh Pantami

Rarara Ya Ƙara Haska Farin Jinin Sheikh Pantami

July 31, 2026

~~~~~~~
Waɗansu matasa huɗu, majiya ƙarfi sun tashi daga Kano suka hau tirela suka tafi Legas da nufin neman aikin ƙarfi.

Yanzu wani abokina, Hon. Mohammed Fayama Jarimi ya turo mini hoton yaran nan, ya ce sun same su ne suna gararamba a kan babbar hanyar nan ta Legas zuwa Ibadan.

Ya ce yaran sun ce su ‘yan Jihar Kano ne a Unguwar Fagge. Sun je Kwanar Dawaki suka ba da Naira 5,000 aka ɗauko su a tirela domin su je Legas su nemi ƙwadago.

Ya ce yaran sun tara Naira dubu biyar ne ta hanyar sayar da ruwan leda da suke yi a Kano.

Fayama, ya ce yanzu haka yaran suna wajensu, sun saya masu abinci, duba da yanayin da suka same su na jigata.

Ya ce ɗaya yaron ya ce mamansa ta rasu amma babansa yana Unguwar Fagge. Ɗaya kuma ya ce auren babansa da mamansa ya mutu, yanzu haka mahaifiyarsa tana Jihar Yobe, inda take aure a can.

Ya ce yaran suna da ƙarancin shekarun da bai kamata a ce sun taho Legas cirani ba.

Mutum zai yi mamakin ko kwana nawa yaran nan suka yi a hanya a cikin tirela, ko yaya suke yi su ci abinci!

Akwai wani matashi mai ƙarancin shekaru da ya taɓa faɗa min cewa ya biyo tirela daga Kano zuwa Legas. Sai da suka shafe sama da kwana 30 a hanya kafin su isa Legas. Ya ce direban da ya biyo, kayan laifi ya ɗauko, din haka cikin sanɗa yake tafiya. A haka sai da suka shafe kwanaki 30 kafin su iso Legas.

A gaskiya ana cikin wani hali, ta yadda yara masu ƙarancin shekaru suke samun kansu cikin mawuyacin hali. Ya kamata duk mahaifin da Allah Ya ba shi ‘ya’ya, ya tabbatar ya riƙe amanar da Allah Ya ɗora masa, wajen ba su kulawa daidai gwargwadon ikonsa. Amma yin watsi da yara abu ne mai matuƙar hatsarin gaske.
~~~~~~~

Previous Post

BINTA OLA: Allah Ji Ƙan Ki Da Rahama

Next Post

MATSALAR TSARO: Sakkwatawa Mu Aje Siyasa Don Fuskantar Wannan Babbar Matsala

Related Posts

Ɗalibin Jami’ar Sojoji Ya Ƙera Robot Mai Kashe Gobara
Babban Labari

Ɗalibin Jami’ar Sojoji Ya Ƙera Robot Mai Kashe Gobara

August 12, 2026
Rarara Ya Ƙara Haska Farin Jinin Sheikh Pantami
Babban Labari

Rarara Ya Ƙara Haska Farin Jinin Sheikh Pantami

July 31, 2026
Janar Buratai Babban Ɗan Kishin Ƙasa Ne – Oba Adekunle Makama
Babban Labari

Janar Buratai Babban Ɗan Kishin Ƙasa Ne – Oba Adekunle Makama

July 30, 2026
Next Post
MATSALAR TSARO: Sakkwatawa Mu Aje Siyasa Don Fuskantar Wannan Babbar Matsala

MATSALAR TSARO: Sakkwatawa Mu Aje Siyasa Don Fuskantar Wannan Babbar Matsala

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

RAMADAN KARIM: 11-1447

RAMADAN KARIM: 11-1447

February 28, 2026
Turning Point Against Terror: The Fall of Abu-Bilal Al-Minuki

Turning Point Against Terror: The Fall of Abu-Bilal Al-Minuki

May 18, 2026
TSAKANIN IRAN DA ISRA’ILA: ANNABI (SAW) YA YI GASKIYA

TSAKANIN IRAN DA ISRA’ILA: ANNABI (SAW) YA YI GASKIYA

June 14, 2025
Ƙasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Yi Tir Da Hare-Haren Sojojin Isra’ila A Zirin Gaza

Ƙasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Yi Tir Da Hare-Haren Sojojin Isra’ila A Zirin Gaza

November 15, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Katsina A Makon Jiya (17-23-08-2026)
  • Professor Bello Sa’idu: The Demise of Literary Icon
  • Bankwana Da Jigon Adabi: Ta’aziyyar Farfesa Bello Sa’idu

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Katsina A Makon Jiya (17-23-08-2026)

Katsina A Makon Jiya (17-23-08-2026)

August 24, 2026
Bankwana Da Jigon Adabi: Ta’aziyyar Farfesa Bello Sa’idu

Professor Bello Sa’idu: The Demise of Literary Icon

August 23, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.