TALAUCI: Yadda Matasan Arewa Ke Gararamba A Legas A Wulaƙance
Daga Abbas Ibrahim Ɗalibi
~~~~~~~
Waɗansu matasa huɗu, majiya ƙarfi sun tashi daga Kano suka hau tirela suka tafi Legas da nufin neman aikin ƙarfi.
Yanzu wani abokina, Hon. Mohammed Fayama Jarimi ya turo mini hoton yaran nan, ya ce sun same su ne suna gararamba a kan babbar hanyar nan ta Legas zuwa Ibadan.
Ya ce yaran sun ce su ‘yan Jihar Kano ne a Unguwar Fagge. Sun je Kwanar Dawaki suka ba da Naira 5,000 aka ɗauko su a tirela domin su je Legas su nemi ƙwadago.
Ya ce yaran sun tara Naira dubu biyar ne ta hanyar sayar da ruwan leda da suke yi a Kano.
Fayama, ya ce yanzu haka yaran suna wajensu, sun saya masu abinci, duba da yanayin da suka same su na jigata.
Ya ce ɗaya yaron ya ce mamansa ta rasu amma babansa yana Unguwar Fagge. Ɗaya kuma ya ce auren babansa da mamansa ya mutu, yanzu haka mahaifiyarsa tana Jihar Yobe, inda take aure a can.
Ya ce yaran suna da ƙarancin shekarun da bai kamata a ce sun taho Legas cirani ba.
Mutum zai yi mamakin ko kwana nawa yaran nan suka yi a hanya a cikin tirela, ko yaya suke yi su ci abinci!
Akwai wani matashi mai ƙarancin shekaru da ya taɓa faɗa min cewa ya biyo tirela daga Kano zuwa Legas. Sai da suka shafe sama da kwana 30 a hanya kafin su isa Legas. Ya ce direban da ya biyo, kayan laifi ya ɗauko, din haka cikin sanɗa yake tafiya. A haka sai da suka shafe kwanaki 30 kafin su iso Legas.
A gaskiya ana cikin wani hali, ta yadda yara masu ƙarancin shekaru suke samun kansu cikin mawuyacin hali. Ya kamata duk mahaifin da Allah Ya ba shi ‘ya’ya, ya tabbatar ya riƙe amanar da Allah Ya ɗora masa, wajen ba su kulawa daidai gwargwadon ikonsa. Amma yin watsi da yara abu ne mai matuƙar hatsarin gaske.
~~~~~~~













