TSAKANIN IRAN DA ISRA’ILA: ANNABI (SAW) YA YI GASKIYA
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
A wannan zamani da muke ciki, babu shakka ya zama dole ga al’ummar Musulmi mu yi alfahari da nuna goyon baya ga ƙasar Iran da masu mulkinta, musamman yadda suke tsaye cikin izza, domin kare martabar Musulmin Duniya daga zaluncin k+firai.
A zahiri, idan ka cire ƙasar Iran, sauran ƙasashen Musulmi suna yin ɗari-ɗari wajen yin fito-na-fito da azz+luman duniya da ke yaƙar Musulunci da Musulmi.
Manzon Allah (saw) shugaban masu gaskiyar kowane zamani, an ruwaito shi yana magana a kan Iran dangane da taimakon Musulunci
Annabi (SAW) ya ambaci mutanen Farisa da yabo a hadisin Sahih Muslim (mai lamba 2546), yana cewa: “Ko da kuwa addini zai kasance a tauraron Surayya (wato a wani wuri mai nisa), mutanen Farisa za su kai gare shi (su kawo shi gida).”
A yau muna ƙara ganin fassarar wannan hadisi, inda ƙasar Iran ce jigo kuma tsinin mashi mai kaifin tsokale idanun K+FIRAN DUNIYA.
A zamunan da suka gabata a baya ma, mun ga fassarar wannan hadisin, domin kuwa mun ji labarin yadda mutane daga yankin Farisa (Iran a yau) suka taimaki addinin Musulunci, musamman ta hanyar ilmantarwa, bincike, da tsantseni wajen koyon addini.
A tarihance, da dama daga cikin manyan malamai da masanan hadisi, tafsiri, da fiƙihu sun fito ne daga yankin Farisa. Jajirtartun sahabbai, kamar Salmanun Farisi (rta) da manyan malaman duniyar Musulunci, kamar Imam Bukhari, Imam Muslim, Imam Tirmidhi, Imam Nawawi da sauransu.
Babu shakka, abin da Iran take yi a yau, ya ƙara gaskata hadisin Manzo (saw) – cewa za su taka rawar gani wajen kiyaye Musulunci.
__________













