• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Wednesday, April 15, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Adabi

Littafin Bango Ya Tsage: Takaitaccen Tsokaci Da Shawara

Fassarar Things Fall Apart na Chinua Achebe

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
August 28, 2023
in Adabi
4
Littafin Bango Ya Tsage: Takaitaccen Tsokaci Da Shawara

Littafin Bango Ya Tsage

72
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Littafin Bango Ya Tsage: Takaitaccen Tsokaci Da Shawara

Babu shakka, duk mai kishin adabi, dole ya jinjina maka dangane da wannan babban aiki da tuni ya kamata a ce an yi shi. Amma godiya ga Allah da ya zo, a yanzu. Ba a makara ba.

Related posts

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

April 11, 2026
FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

March 7, 2026

Babu wanda zai kushe wannan aiki, sai wanda ya kawo ƙyashi da hassada. Don haka ya kamata tsangayoyin Hausa na jami’o’i da kwalejojin ilimi na duniya su amshi wannan aiki da kyau sosai.

Wannan babban aiki yana ɗauke da muhimman abubuwa guda biyu: Bunƙasa Adabin Hausa da na Afirka da kuma kawo fahimta tsakanin al’adun Hausawa da na Ibo.

Ya kamata marubutanmu na Hausa su ɗauki hannu, su nitsa cikin binciken al’adunmu na dauri na cikin gida, su samar da manyan litattafai na alfahari irin wannan. Ba kawai a tsaya kallon finafinan Indiya ana kwafowa ana maka wa Hausawa ba. Idan muka tsaya ga littattafan gaske da marubutan Afirka suka samar, za mu gina namu masu inganci da amfani ga al’umma.

Malam Ibrahim Sheme , ina da ‘yan shawarwari guda biyu game da wannan babban aiki naka.

1-A fahimtata sunan littafin nan: “Bango Ya Tsage” bai kamaci fassarar “Things Fall Apart” ba, musamman idan muka duba ma’anar karin maganar ‘sai bango ya tsage ƙadangare ke samun wurin shiga.’ Shi tauraron littafin Things Fall Apart, tun da farko ba wani bango ba ne. Hasalima ya faro haƙilon rayuwarsa daga tushe – bai da gatan komai. Don haka, ina ba da shawara da a ƙara nazari a samo sunan da ya dace, duk kuwa da cewa BANGO YA TSAGE yana da daɗi da kama fuska, to amma ma’anarsa ba ta dace da ƙunshiyar littafin ba.

2-Shawara ta biyu, ita ce game da amfani da tsarin Ƙa’idojin Rubutun Hausa. Kowa ya san matsayarka da fahimtar ƙashin kanka game da wasu daga ƙa’idojin rubutun Hausa, musamman abin da ya shafi rabawa ko haɗewar lamurran mallaka.

Ko a can baya, musamman dangane da mashahurin littafinka na ‘YARSANA’ an sha daga da masana Hausa. Babu shakka rashin bin waɗannan ƙa’idoji na bai ɗaya a duniyar manazarta nahawun Hausa, ba ƙaramar naƙasu take kawo wa mashahuran littattafanka ba.

Don haka ina shawartarka da cewa, ya kamata a wannan babban aiki na Bango Ya Tsage, ka daure ka ɗabbaƙa ƙa’idojin nan na bai ɗaya, ka jingine wannan na ƙashin kanka. Ba don gazawa ba, amma domin tafiya da Duniyar Manazarta Hausa. Ina ganin hakan zai ƙara wa aikinka martaba a DUNIYAR HAUSA.

Ina fatan za ka kalli shawarwarin nan da idon basira, a matsayin gudunmawata ga kishin adabin Hausa da rubutunsa.

Ina yi maka fatan alheri da fatan littafin nan zai amfani al’umma, amin.
~~~~~~~
Daga Bashir Yahuza Malumfashi
Babban Editan Jaridar Taskar Gizago
~~~~~~~

Previous Post

Bakan Gizo

Next Post

YAMTARAWALA Ya Kama Hanyar Lashe Gasar Adabi Ta NLNG

Related Posts

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza
Adabi

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

April 11, 2026
FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)
Adabi

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

March 7, 2026
Let’s Speak Our Mother Tongue
Adabi

Mu Yi Kishi Da Alfahari Da Harshen Uwa

March 6, 2026
Next Post
YAMTARAWALA Ya Kama Hanyar Lashe Gasar Adabi Ta NLNG

YAMTARAWALA Ya Kama Hanyar Lashe Gasar Adabi Ta NLNG

Comments 4

  1. Musa Ibrahim says:
    3 years ago

    Na karanta shawarwarinka, kuma gaskiya sun zo daya da nawa. Kuma ni ma a shafinsa na Facebook na gaya masa shawararka ta farko.

    Reply
    • Bashir Yahuza Malumfashi says:
      3 years ago

      Haka ne. Allah kara mana fahimta. Na gode sosai.

      Reply
  2. Ibrahim Sheme says:
    2 years ago

    Salaam.
    Sai yanzu na dawo kan wannan shawarar da ka kawo a kan littafin Bango Ya Tsage. A lokacin da ka yi ta, aiki ya rufe ni, kuma an yi “comments” masu ɗimbin yawa a kan rubutun da na yi a Facebook waɗanda ba zan iya amsa su ɗaya bayan ɗaya ba.

    1. Ba shakka, sunan da na ba littafin a fassara shi ya fi dacewa da shi. Ba za ka fahimci dacewar fassarar sunan littafin ba har sai ka san ma’ana da manufar sunan da Chinua Achebe ya raɗa wa nasa littafin, da kuma inda ya ɗauko sunan. Akasin yadda ka ce, ba Okonkwo ba ne “bango” a labarin. “Bango” na nufin ita al’ummar Ibo a lokacin da Turawan mishan da na mulkin mallaka suka kutsa kai a ƙasar. Okonkwo ya so a ce al’ummar sa sun cure sun zama tsintsiya maɗaurin ki ɗaya, kada su rarraba, domin su yaƙi kutsen da Turawan suka yi masu, suka wargaza su, suka kawo masu baƙin al’adu da addini. Hausawa sun ce “sai bango ya tsage ƙadangare ke samun wurin shiga.” A littafin Things Fall Apart na Achebe, “bangon” (wato al’ummar Ibo) ya tsage ne, shi ya sa “ƙadangare” (wato Turawa) suka samu har suka kurɗa cikin su, suka kawo masu rarrabuwar da ta jawo masu faɗa da junan su. Wannan rarrabuwar ita ce “things fall apart” – wato abubuwa sun tarwatse; al’amurran al’ummar Ibo sun tarwatse!

    A tawa fassarar, na ƙi in ce “al’amurra sun tarwatse” ko “abubuwa sun tarwatse” kamar yadda wasu na ga wasu masu sharhi suka so in ce. Dalili shi ne yin hakan zai karya ƙa’idar yin fassara, wato zai zama “direct translation”. Abin da na yi shi ne “fassara daidai da maudu’i”, wato “contextual translation.”

    A cikin littafin kuwa, na yi ƙoƙari matuƙa wajen bin kalmomi da jumlolin magana na Achebe na asali sau da ƙafa don tabbatar da cewa ban kauce alƙiblar da ya dosa ba, ko ainihin manufar da yake so ya isar ga mai karatu. Na tabbatar za ka fahimta yanzu.

    2. Ƙa’idojin Rubutu: ???

    Ibrahim Sheme
    15 ga Agusta 2024

    Reply
    • Bashir Yahuza Malumfashi says:
      2 years ago

      VeGA SHAWATA TA BIYU:

      Malam Ibrahim Sheme , na gamsu da bayaninka sosai dangane da shawarata ta 1.

      Amma dangane da shawara ta 2, ina ganin kamar ka samu tangarɗa wajen kwafo sharhin nawa duka, daga ainahin shafin Taskar Gizago , ka ɗauko iyaka shawarata ta 1, ka bar ta biyu.

      To ga ta biyun nan kamar yadda na bayyana tun da farko:

      ~~~

      2-Shawara ta biyu, ita ce game da amfani da tsarin Ƙa’idojin Rubutun Hausa. Kowa ya san matsayarka da fahimtar ƙashin kanka game da wasu daga ƙa’idojin rubutun Hausa, musamman abin da ya shafi rabawa ko haɗewar lamurran mallaka.

      Ko a can baya, musamman dangane da mashahurin littafinka na ‘YARSANA’ an sha daga da masana Hausa. Babu shakka rashin bin waɗannan ƙa’idoji na bai ɗaya a duniyar manazarta nahawun Hausa, ba ƙaramar naƙasu take kawo wa mashahuran littattafanka ba.

      Don haka ina shawartarka da cewa, ya kamata a wannan babban aiki na Bango Ya Tsage, ka daure ka ɗabbaƙa ƙa’idojin nan na bai ɗaya, ka jingine wannan na ƙashin kanka. Ba don gazawa ba, amma domin tafiya da Duniyar Manazarta Hausa. Ina ganin hakan zai ƙara wa aikinka martaba a DUNIYAR HAUSA.

      Ina fatan za ka kalli shawarwarin nan da idon basira, a matsayin gudunmawata ga kishin adabin Hausa da rubutunsa.

      Ina yi maka fatan alheri da fatan littafin nan zai amfani al’umma, amin.
      ~~~~~~~
      Daga Bashir Yahuza Malumfashi
      Babban Editan Jaridar Taskar Gizago
      ~~~~~~~

      Reply

Leave a Reply to Bashir Yahuza Malumfashi Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

KUSKUREN MASU JUYIN MULKIN KASAR NIJAR

KUSKUREN MASU JUYIN MULKIN KASAR NIJAR

August 9, 2023
Tinubu Ya Ƙwace Muƙamin Minista Daga Maryam Shatty

Tinubu Ya Ƙwace Muƙamin Minista Daga Maryam Shatty

August 4, 2023
TAURARON GIZAGAWA: ABDULHADI DABO

TAURARON GIZAGAWA: ABDULHADI DABO

July 20, 2023

October 1, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye
  • Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
  • MARTABAR MANZON ALLAH (SAW)

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

April 14, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.