TAURARON GIZAGAWA: ABDULHADI DABO
A wannan lokaci, Abdulhadi Dabo, Sardaunan A Bari Ya Huce, shi ne ya kasance Tauraron Gizagawa.
Wane Ne Abdulhadi?
An haifi Abdulhadi a cikin garin Zariya da ke Jihar kaduna.
Ya yi karatun Firamare da Sakandare duk a Jihar Kaduna, inda ya samu shaidar digiri na ɗaya da na biyu. Yanzu haka kuma yana kan neman digiri na uku a fannin Kimiyyar Sarrafa Bayanai (Management Information Systems). Yana da aure da kuma yara.
Matsayinsa A Gizago:
Abdulhadi Dabo, shi ne mai Lambar Gizago GZG-035-KDN. Yana daga cikin mutane uku da suka ƙarfafa aka kafa Ƙungiyar Gizago Ta Nigeria. Hasali ma, shi ne Shugaban ƙungiyar Gizago na ƙasa na farko, wanda ya taimaka sosai wajen tabbatar da haɗin kai da zumunci tsakanin Gizagawan Nigeria.
Fahimtarsa Game Da Zumunci:
“Zumunci abu ne mai kyau, kuma ni da sauran Gizagawa duk mun ga amfaninsa. Sanadiyyar zumunci ne yanzu ya sa muka zama ‘yan uwan juna tsakaninmu Gizagawa. Domin babu inda za ka je, in dai akwai Bagizage ba za a amshe ka da mutunci ba. In dai ka sauka hannun ‘yan uwa, za karrama ka kuma za a yi maka hidima. Haƙiƙa zumunci yana da amfani sosai.”
Tsokacinsa Game Da Gizago:
“Game da Ƙungiyar Gizago kuwa, gaskiya sai dai in ce Alhamdu lillahi. Haka kuma muna gode wa Malam Bashir Yahuza Malumfashi tare da Jaridar Aminiya, kan taimakawa da suka yi wa wannan ƙungiya da kuma ‘ya’yanta.
“Sanadin Gizago ya sa yanzu mun zama ‘yan uwan juna da mafi yawancin mambobinmu.
Babu inda wata hidima ta Bagizage ko Bagizagiya zai taso da ba za ka ga mun yi cincirindo mun je ba. Sanadin ƙungiyar Gizago an samu Gizagawa da suka auri junansu, wasu kuma suka ƙulla kasuwanci da dai sauransu. Gaskiya babu abin da zan ce sai dai alhamdu lillahi. Da fatan za mu ci gaba da zumunci a kodayaushe.”
Shawararsa Ga Gizagawa:
1-Mu riƙa kyautata ikhilasi a kan ayyukanmu.
2-Mu ci gaba da haƙuri da juna.
3-Mu dage da zumunci da muke yi, kada mu ja baya.
4-A ci gaba da taimakon juna a duk inda ya kamata.
5-Kada mu yi ƙasa a gwiwa wajen yi wa Malam Bashir Yahuza Malumfashi da jaridar Aminiya addu’ar samun nasara a kodayaushe.













