MARTABAR MANZON ALLAH (SAW)

__________
Muhammadu (Sallallahu Alaihi Wasallam), Manzon Allah ne kuma shi ne cikamakin manzanni. Darajarsa ta fi kowace halitta daraja kuma wajibi ne ga kowane Musulmi ya kare martaba da darajarsa.
Abin baƙin ciki ne kuma abin Allah wadai ne da a yau aka samu wani gafalalle yana tozarta ƙima da darajarsa. Haka kuma wajibi ne, haƙƙi ne ga kowane Musulmi ya yi Allah wadai da wannan fasto da ya aikata wannan mummunan aiki.
Muna kira ga hukumomi da su ɗauki matakin da ya dace a kansa tare da gargaɗin duk wani mai gigin son aikata irin haka.
Muna roƙon Allah ya daɗa tsira da aminci da martaba ga fiyayyen talikai, badadin Allah, Annabi Muhammadu (saw). Kuma Allah, cikin ikonka da izzarka, Allah ka tozarta duk wani mai tozarta manzonka. Allah ka wulaƙanta shi tun a nan duniya. Amin-Summa-Amin.
__________












