REGINA OGECHUKWU: Abubuwan Da Na Fahimta Daga Littafin Girl-Child Education in Biu Emirate


~~~~~~~
Sunan Littafi: Girl-Child Education in Biu Emirate (The Early Years)
Sunan Marubuci: Dr. Bukar Usman, OON
Kamfanin Wallafa: Klamidas Communication Ltd. Abuja
Shekarar Wallafa: 2014
Yawan Shafukan: 136
Mai Sharhi: Regina Ogechukwu Nwangele
Lambar ISBN: 978-978-52655-9-0
~~~~~~~
Littafin Girl-Child Education in Biu Emirate (The Early Years), littafi ne da ke ƙunshe da bincike da nazari da sharhi iri-iri, dangane da tarihi, gwagwarmaya da faɗi-tashin da mata suka sha domin samun ilimin zamani, musamman a tsakanin shekarun 1930 zuwa 1950. Kodayake bayanan sun taƙaita ga matan Masarautar Biu da ke Jihar Borno, amma misalai da darussan da aka tattauna za su iya shafar ko’ina a duniyar baƙar fata, ba ma Arewacin Nigeria kaɗai ba.
Littafin ya yi bayanin irin gwagwarmayar da matan suka yi na yaƙi da wariyar jinsi, yaƙi da ko’in kula daga iyaye, dangane da ilimin ‘ya’ya mata da yaƙi da auren wuri, wanda ke takura su, su gaza samun ilimin zamani, kamar takwarorinsu mata.
Ya kuma samar da faffaɗan bayanin yadda matan suka jajirce, suka fuskanci kowane ƙalubale, har sai da suka samu nasarar kasancewa mata na sahun farko da suka samu ilimin zamani a cikin al’ummarsu. Suka samu nasarar zama abin kwatance da misali, wajen kawo canji da ci gaba na alheri a yankunansu. Wasu daga cikin irin waɗannan matan, sun riƙa jure wa tafiya a ƙasa, sukan share tafiyar Kilomita 24 a ƙasa, a duk lokacin da aka yi masu hutu, domin zuwa gida daga makaranta. Sannan kuma idan lokacin komawa makarantar ya yi, haka dai za su taka a ƙasa. Akwai ma labarin wata yarinya daga cikinsu, ‘yar shekara 8, wacce ta abauce wa ra’ayin iyayenta, ta kai kanta makaranta.
Babban dalilin rubuta wannan littafi ya ta’allaƙa ne da irin kishin da Dokta Bukar Usman yake da shi, na ganin cewa mata sun samu ingantaccen ilimin da ya dace da su. Dalili ke nan ma ya samu shaidar kai tsaye daga bakunan wasu daga cikin matan da har yanzu suke raye, inda suka bayyana irin nasarorin da suka samu a rayuwa, biyo bayan ilimin da suka samu. Wannan ke ƙara tabbatar da cewa, lallai babu abin da ya kai ilimantar da mata ƙima, musamman wajen yaƙi da jahilci, yaƙi da talauci kuma domin samar da al’umma mai wayewa, mai arziƙi, mai lafiya da zaman lafiya.
Regina Ogechukwu Nwangele, ɗaliba ce da ba ta daɗe da kammala karatu a Jami’ar Nsukka a farkon shekarar nan ba. Ta samu digirinta na farko a fannin Ilimin Zamantakewar Ɗan Adam da kuma Nazarin Rayuwa da Al’adu. A yanzu haka tana zaune a garin Aba na Jihar Abiya. Ta samu zarafin karantawa tare da nazarin wannan littafi na Girl-Child Education in Biu kuma ya ɗauki hankalinta matuƙa. Dalili ke nan ma ta rubuta taƙaitaccen sharhi dangane da abubuwan da ta fahimta daga gare shi kuma ta aiko wa marubucinsa.
Da gaisuwa ta buɗe sharhin nata, inda ta ce: “Barka da wannan lokaci Dokta, da fatan ka shiga sabon wata cikin ƙoshin lafiya. A yanzu haka ina kan hanya daga Jihar Taraba zuwa Kudu Maso Gabas, kasancewar mun kammala Share Fagen Hidimar Ƙasa (NYSC), a ranar Talata da ta gabata.
“Na yi katarin karance littafinka mai taken Girl-Child Education in Biu Emirate: The Early Years, a yayin da nake kan tafiya zuwa gida. Babu shakka wannan littafi ƙayatacce ne, gwanin daɗin karantawa. Sai dai ni a nazarin da na yi kuma a ra’ayina, sunan Viyu ya fi kyau kuma ya fi daɗin faɗa, idan aka kwatanta da Biu.
“Wannan littafin ya fayyace girma da ƙimar Masarautar Biu. Babu shakka ingantattu kuma sahihan bayanan da aka fayyace a littafin gamsassu ne kuma na yaba matuƙa da aikin. An yi namijin ƙoƙari wajen tattaro sahihan bayanai, kai tsaye daga matan da suka fara samun ilimin zamani a Biu da ma wajen Jihar Borno. Haka kuma an bayyana irin ƙoƙari da jajircewar da matan suka yi, a hanyarsu ta neman ilimi.
“Haka kuma, wani abin da na fahimta shi ne, har a rayuwarmu ta yau, ana samun wannan yanayi na nuna ƙyama da bambanci ga karatun mata, a yankunan karkara. Sai dai kuma matsalar ta fi ƙamari ga yara maza da mata, a inda aka samu gwamnati da iyayen da ke nuna halin ko’in kula da ilimi.
“A cikin jaruman matan nan 21 da aka baje kolin bayanansu a littafin nan, hankalina ya fi ɗaukuwa ga waɗannan jajirtattun. Su ne Hadiza Shettima Pindar da Caca Betara Garga Biu da Sindiwa Tasiwa da kuma Jummai Diggira. Gaba ɗayan matan 21 sun jajirce, sun sanya himma domin neman ilimi, duk kuwa da irin ƙalubalen da al’ummarsu suka gindaya masu.
“Ya zama wajibi in jinjina maka kuma in yi maka godiya, bisa himma da ƙoƙarinka na ganin mata sun samu ilimi. Haka kuma da irin yadda ka gano irin ƙima da mutuncin matan Biu da ma na Nigeria baki ɗaya. Ina roƙon Allah Mai Girma da Ɗaukaka Ya ci gaba da sanya wa kyakkyawar zuciyarka albarka, Ya ƙara maka hikima da basira da ingantattar lafiyar zuciya da ta jiki. Na gode matuƙar gaske da karimcinka, da ka ba ni kyautar wadannan littattafai naka.
“Ni ce mai yi maka fatan alheri. – Regina Ogechukwu Nwangele.”
Game da marubucin kuwa, Dokta Bukar Usman, D.Litt, M.IoD, OON, an haife shi a garin Biu, Jihar Borno a ranar 10 ga watan Disamba, 1942. Ya yi karatun zamani tun daga Firamare har zuwa Digiri a fannin tafiyar da gwamnati da hulɗa da ƙasashen waje, a Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya. Ya yi aikin gwamnati tun daga ƙaramin ma’aikaci daga 1965, har ya kai muƙamin Babban-Sakare a Fadar Shugaban Ƙasa, inda ya kammala aiki a shekarar 1999. Ya rubuta littattafai sama da guda 40 a fagagen ilimi daban-daban. Shi ne Shugaban Gidauniyar Bukar Usman, wacce ya kafa domin jin ƙan raunana, bunƙasa ilimi da sauransu. Haka kuma shi ne Shugaban Ƙungiyar Nazarin Al’adun Gargajiya ta Najeriya (NFS).
~~~~~~~













