Birgediya-Janar Sani Usman Kuka-Sheƙa (mai ritaya), shi ne Sarkin Yaƙin Kanwan Katsina, kamar kuma yadda ya kasance tsohon Kakakin Rundunar Sojojin Najeriya. Yana daga cikin na hannun daman tsohon Ambasadan Najeriya a Jamhuriyar Benin, Laftanar-Janar Tukur Yusuf Buratai (mai ritaya), OFR, Betaren Biu kuma Garkuwan Keffi. A wannan rahoto na musamman, Janar SK Usman ya bayyana yadda suka ziyarci Daura a makon nan:
A ranar Juma’ar da ta gabata (02-06-2023) na samu martabar yin rakiya ga Mai Girma Laftanar-Janar Tukur Yusuf Buratai (mai ritaya) CFR (Magayakin Ƙasar Hausa), tsohon Babban Hafsan Rundunar Sojojin Najeriya, tsohon Ambasadan Najeriya a Jamhuriyar Benin, zuwa birnin Daura mai daɗaɗɗen tarihi, a Jihar Katsina, Najeriya.
Maƙasudin ziyarar shi ne domin gaisuwa ta musamman ga babban ɗan kishin ƙasa, dattijo, tsohon Shugaban Ƙasa, Mai Girma Janar Muhammadu Buhari, GCFR kuma domin taya shi murnar kammala shugabancin Najeriya na tsawon shekaru takwas. Haka kuma mun yi masa fatan alheri da addu’ar ci gaba da samun nasara a rayuwarsa ta gaba. Haka kuma mun yi masa godiya da irin goyon baya da tagomashi da ya riƙa bai wa Janar Buratai, a lokacin shugabancin Rundunar Sojojin Najeriya. Mun yaba masa da irin yadda ya yi wa al’ummar Najeriya da ma duniya baki ɗaya hidima a tsawon shekarun mulkinsa.
Irin wannan muhimmiyar ziyara ba za ta kammala ba, ba tare da mun miƙa gaisuwa ta musamman ga Uban Ƙasa, Mai Martaba Sarkin Daura, Farouk Umar Farouk CFR ba. Don haka, wannan ziyara ta ba mu damar gabatar da Sallar Juma’a a babban masallacin Daura tare da Mai Martaba Sarki da Shugaba Buhari, sannan kuma muka ziyarci fadarsa.
Babu shakka, wannan ziyara ta ƙayatar da mu, musamman yadda ta farfaɗo mana da tarihin wannan muhimmin gari da masarauta da ta share sama da shekaru 3,000 a duniya. Wani al’amari muhimmi da ya ɗauki hankalina, shi ne irin kaifin basirar Mai Martaba Sarki da irin karsashinsa da kula da mu cikin karimci, duk kuwa da cewa ya cin ma shekara fiye da 91. Mun yi amfani da wannan dama wajen yabawa da nuna matuƙar godiyarmu da irin karimcin da ya nuna mana da ƙauna, a matsayinsa na uban al’umma.
A duk tsawon ziyarar nan tamu, an nuna mana tsantsan karimci, gami da ingantaccen abincin rana, wanda Alhaji Mamman Daura da Ambasada Muntari Ali Daura suka tanadar mana. Abokina Alhaji Rabe, sai da ya tanadar mani da sanannar “fura da nonon Daura” domin kawo tsaraba Abuja.
Babu raba ɗaya biyu, tabbas wannan ziyara za ta daɗe a zuciyata, a matsayin ɗaya daga zumunci mafi fa’ida da suka faru a rayuwata. Babu shakka na ƙaru da ilimi da zumunci da ƙauna, kamar yadda ta ƙarfafa mani gwiwar ci gaba da riƙe halayen gaskiya da amana. Lallai na ji daɗin wannan ziyara mai girma da muhimmanci, wacce ba zan iya ƙimanta ta da komai ba.


















