• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, September 10, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

TARON MALUMFASHI FACEBOOK CONNECT: YUNKURIN BUNKASA MALUMFASHI DA KEWAYE (8)

BABBAN LABARI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
October 13, 2025
in Babban Labari
0
TARON MALUMFASHI FACEBOOK CONNECT: YUNKURIN BUNKASA MALUMFASHI DA KEWAYE (8)

Injiniya Tukur Hassan Tingilin, FNSE

37
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

TARON MALUMFASHI FACEBOOK CONNECT: YUNKURIN BUNKASA MALUMFASHI DA KEWAYE (8)

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Wane Ne Ya Kashe Ɗan Shagamu?

Wane Ne Ya Kashe Ɗan Shagamu?

September 9, 2026
Ƙauna: Budurwa Mai Bautar Dodo Ta Musulunta

Ƙauna: Budurwa Mai Bautar Dodo Ta Musulunta

September 3, 2026
Zannan Galadima, Injiniya Tukur Tingilin, a yayin jawabi a zauren karrama DPO na Malumfashi, CSP Bello Umar da sauran masu taimakon al’umma ta fuskar tsaro a Malumfashi da kewaye

 

                       _______________

Jama’a masu bibiyar wannan rahoto mai kama da muƙala, wannan shi ne rahoto kashi na 8, dangane da wannan babban taro da aka gudanar na Malumfashi Facebook Connect. Idan ba mu mance ba, an gudanar da taron ne a ranar Lahadi, 12-12-1446 (Hijiriyya), 08-06-2025 (Miladiyya).

Kamar yadda muka yi alƙawari, a wannan rahoton za mu yi bayani ne game da ɗaya daga cikin jajirtattun mutanen da aka karrama a wannan taron. Wannan kuwa shi ne Manajan Darakta na Hukumar Ruwa ta Jihar Katsina, Dokta Tukur Hassan Tingilin, FNSE.

√ Wane Ne Dokta Tukur Tingilin?

Tukur Hassan Tingilin. An haife shi ne a Unguwar Tingilin Malumfashi, Ƙaramar Hukumar Malumfashi, Jihar Katsina, a ranar Asabar – 4 ga Rajab, 1398 (Hijiriyya), daidai da 10 ga Yuni, 1978 (Miladiyya). Ya yi karatu mai zurfi, tun daga firamare, har zuwa matakin da ya samu Digirin Digirgir (PhD) a fannin Injiniya da ya shafi Ilimin ƙarafa (Mechanical Engineering). Ya yi gwagwarmayar neman ilimi a wurare da dama a cikin Najeriya da ƙasashen waje, musamman ma dai ƙasar China, inda a can ya yi karatun Digiri na biyu da na uku.

Injiniya Tingilin hadimin jama’a ne. Ya yi aikin koyarwa, kamar kuma yadda ya kasance mai fafutukar taimakon al’umma ta hanyar ƙungiyoyin sa-kai na tallafa wa al’umma. Haka kuma shi ɗan siyasa ne, wanda ya sadaukar da kansa domin hidima wa jama’arsa. A yanzu haka, shi ne Manajan Darakta na Hukumar Ruwa ta Jihar Katsina.

A hagu, Dokta Tingilin yana gaisuwa ga Galadiman Katsina, Hakimin Malumfashi, Mai Shari’a Sadiƙ Abdullahi Mahuta

√ Dalilin Karrama Dokta Tingilin:

Ba Injiniya Tukur kaɗai ba, dukkan waɗanda aka karrama a wannan taro, mutane ne da sunansu ya buga tambari wajen taimakon al’umma a Malumfashi da kewaye, kamar mutane irin su Dokta Bala Funtua, Injiniya Muntari Sagir, Jibrin Sama’ila Jibson, Haruna Musa Rugoji da sauransu. Don haka an karrama Injiniya Tukur Tingilin a wannan taro ne bisa cancanta.

A hagu, Injiniya Tingilin, a yayin tattauna al’amuran tsaro

Tun ma kafin ya kai ga hawa wannan muƙami na Manajan Darakta a Gwamnatin Malam Dikko Umar Raɗɗa, duk wanda ya san shi, ya san mutum ne shi da ya saba da gudanar da ayyukan tallafa wa al’umma, musamman ma ta fuskar aikin gayya, ilimi da abin da ya shafi tallafi ga majinyata a asibitocinmu.

Ya zuwa yanzu, maganar gaskiya ba za a iya lissafa irin yawan tallafi da gudunmawar da Dokta Tingilin yake bayarwa ga al’umma ba, musamman ma ta hanyar gidauniyarsa ta Zanna-Wali Foundation. Duk fannin da ka duba, abin da ya kama da ɓangaren tsaro, harkar lafiya, ruwan sha, ilimi da kuma tallafin kuɗi kai tsaye ga mabuƙata, Injiniya yana yin iyaka ƙoƙarinsa.

A hagu, Injiniya Muntari Sagir tare da Alhaji Jibrin Sama’ila Jibson, a zauren taron Malumfashi Facebook Connect

Wata babbar ɗabi’a aka shaidi Dr. Tingilin da ita, ita ce ɗabi’ar jajircewa da ƙoƙarin neman na kansa. Yana da karimci da kara. Yana girmama mutane kuma ba ya ramuwar gayya.

Waɗannan dalilai da ma wasunsu da dama, su ne dalilan da suka sanya ya kasance ɗaya daga cikin zaratan mutanen Malumfashi da aka karrama a wannan babban taro. A lokacin da za a miƙa masa kambin karramawa, ba ya wajen taron, domin kuwa a lokacin yana ƙasa mai tsarki, Makka, wajen aikin Hajji. Muna yi masa fatan alheri.

A dama, Alhaji Jibrin Sama’ila Jibson ne yake amsar kambi daga Shugaban Ƙaramar Hukumar Malumfashi, Alhaji Mukhtar Abdullahi, a zauren taron

Ina sha Allahu, a rahoto na gaba, kashi na 9, za mu tattaunawa a kan DPO na Malumfashi, CSP Bello Umar, wanda shi ma aka karrama, saboda gudunmawarsa ta fuskar tsaro a Malumfashi da kewaye.
_______________

Previous Post

Sasanci Da ‘Yan Bindiga: A Sake Duba Lamarin Nan A Tsanaki

Next Post

Bayan Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihar Katsina: Ya Kamata A Tallafa Wa Iyalan Mutanen Da Aka Tarwatsa

Related Posts

Wane Ne Ya Kashe Ɗan Shagamu?
Babban Labari

Wane Ne Ya Kashe Ɗan Shagamu?

September 9, 2026
Ƙauna: Budurwa Mai Bautar Dodo Ta Musulunta
Babban Labari

Ƙauna: Budurwa Mai Bautar Dodo Ta Musulunta

September 3, 2026
KATSINA_2026: Bikin Ranar Marubutan Hausa ta Duniya
Babban Labari

KATSINA_2026: Bikin Ranar Marubutan Hausa ta Duniya

August 29, 2026
Next Post
Bayan Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihar Katsina: Ya Kamata A Tallafa Wa Iyalan Mutanen Da Aka Tarwatsa

Bayan Sulhu Da 'Yan Bindiga A Jihar Katsina: Ya Kamata A Tallafa Wa Iyalan Mutanen Da Aka Tarwatsa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Hajia Amina Donates Mosque Building to Muslim Community

Hajia Amina Donates Mosque Building to Muslim Community

March 11, 2024
FESTIVAL OF AUTHORS KADUNA 2024

FESTIVAL OF AUTHORS KADUNA 2024

October 24, 2024
Ibtila’in Ambaliya Ya Cinye Mace Da Goyonta A Zariya

Ibtila’in Ambaliya Ya Cinye Mace Da Goyonta A Zariya

September 10, 2025
Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

January 14, 2026

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Shugaba Tinubu, Manyan Sojoji, Mutallab, Mangal, Sarki Sanusi II Za Su Halarci Ƙaddamar Da Littafin Janar Buratai
  • Wane Ne Ya Kashe Ɗan Shagamu?
  • SANATA BELLO MANDIYA: Mun Yi Babban Rashi – Gwamnan Katsina

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Shugaba Tinubu, Manyan Sojoji, Mutallab, Mangal, Sarki Sanusi II Za Su Halarci Ƙaddamar Da Littafin Janar Buratai

Shugaba Tinubu, Manyan Sojoji, Mutallab, Mangal, Sarki Sanusi II Za Su Halarci Ƙaddamar Da Littafin Janar Buratai

September 10, 2026
Wane Ne Ya Kashe Ɗan Shagamu?

Wane Ne Ya Kashe Ɗan Shagamu?

September 9, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.