Abdullahi Garba Faskari Ne Sabon Sakataren Gwamnatin Katsina
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa ya amince da naɗin tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Abdullahi Faskari, a matsayin sabon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina.
Tsohon Mataimakin Gwamnan, wanda ya yi mulki a shekarar 2011 zuwa 2015, ya maye gurbin Architect Ahmed Musa Ɗangiwa, bayan Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya naɗa shi Minista a gwamnatinsa.
Gwamna Raɗɗa ya bayyana ta bakin Kakakinsa, Ibrahim Kaula Mohammed, cewa naɗin sabon Sakataren Gwamnatin zai fara aiki nan take.
“Babu shakka, nadin Alhaji Abdullahi Garba a matsayin Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, kamar ajiye ƙwarya ne gurbinta, domin kuwa ya canc” in ji Gwamna Raɗɗa.
An haifi sabon Sakatare Abdullahi Garba a ranar 15 ga Agusta, 1959 a garin Faskari. Ya taɓa zama Kwamishinan Shari’a a Jihar Katsina, a 2003 zuwa 2007, da kuma 2007 zuwa 2009. Sannan kuma ya yi Kwamishinan Ilimi a Jihar Katsina, a 2009 zuwa 2010. Kafin naɗin nasa Sakataren Gwamnati a wannan karon, shi ne Shugaban Hukumar Gudanarwa na Jami’ar Umaru Musa ‘Yar-Adua, Katsina.













