Matsalolin Da Suka Daƙile Super Eagles Daga Gasar Kofin Duniya
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

•••••••
A jiya ne Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta ƙasar DR Congo ta doke Ƙungiyar Super Eagles ta Najeriya, a ƙoƙarinta na samun gurbin fafatawa a Gasar Kofin Duniya da za a gudanar a ƙasar Qatar a baɗi. Matsaloli da yawa sun taka rawa wajen daƙile himmar Super Eagles. Ga wasu daga ciki:
√ Yawan Sauya Ƙwararrun Masu Horar Da Super Eagles:
Ɗaya daga cikin manyan matsalolin da Najeriya ta sha wahala da su, ita ce rashin daidaiton horo. A yayin yaƙin neman gurbi a gasar ta baɗi, Super Eagles sun yi amfani da masu horarwa daban-daban, waɗanda suka haɗa da Peseiro, Finidi George da kuma Eric Sekou Chelle. Wannan rashin daidaito na masu horar da ƙungiyar, ya taka rawa wajen daƙile ƙungiyar daga samun tsarin wasa guda ko salon da aka dogara da shi, wanda ya shafi haɗin kan ‘yan wasa a yayin da suka shiga filin wasa.
√ Ƙarancin Himma da Rashin Mayar da Hankali a Wasanni Masu Matuƙar Muhimmanci:
A wasu lokuta, Super Eagles sun ja wa kansu rashin nasara ko kuma samun sakamako mara kyau a wasansu da ƙungiyoyi da ake ganin ba su da ƙarfi sosai. Misali, sun yi canjaras da ƙasashen Lesotho (1–1), Zimbabwe da kuma asara mai zafi a wasansu da ƙasar Benin, bayan kuma su suka fara da cin ƙwallo. Wannan ya nuna akwai matsalar rashin mayar da hankali a lokutan da ake tsammanin samun nasara cikin sauƙi.
√ Rashin Tsari Daga Gwamnati Da Hukumar Kwallon Ƙafa Ta Najeriya:
Akwai rahotanni cewa Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Najeriya (NFF) ba ta tafiyar da abubuwa yadda ya kamata ba. An ce akwai matsalolin kuɗi, rashin biyan albashi da bashi na horo ga ’yan wasa da ma’aikata da kuma rashin gaskiya da bin ƙa’idoji. Bugu da ƙari, wasu suka nuna cewa NFF ba ta sanya himma ba sosai wurin duba filayen wasa da yanayinsu. Wani rahoto ya ce filin wasa da Najeriyar za ta buga a ƙasar Afirka ta Kudu bai dace ba kuma NFF ba ta yi ƙoƙarin kawo gyara ba. Haka ma wajen zaɓen ‘yan wasa, akwai ƙorafin cewa ana sanya son kai, ƙabilanci da ɓangaranci ko karɓar cin hanci, kafin a saka ɗan wasa a Super Eagles. An nuna cewa, ana zaɓen ‘yan wasa mafi yawa daga Kudu, ana barin ƙwararru da suka fito daga Arewa.
Matsalolin Fasaha a Wasanni:
A ɓangaren wasanni, Super Eagles sun nuna rauni a wasu sassa, musamman wajen kare gidansu (defense) da kuma sarrafa wasan tsakiya. Rahotanni sun bayyana rashin haɗin kai a tsakanin ’yan tsaron ƙungiyar (centre-backs) da matsalolin maki a manyan lokuta. Haka kuma, ba su nuna ƙarfi sosai a wajen kai hari ga abokan hamayya ba; duk da cewa suna da ’yan wasa ƙwararru da ke buga ƙwallo a manyan ƙungiyoyin ƙasashen Turai. Wannan sakaci ya hana su samun maki wadatacce a wasu wasanni.
√ Rashin Nuna Kishin Ƙasa:
A cewar Moses Simon (ɗaya daga cikin manyan ’yan wasan Super Eagles), “akwai buƙatar kowa ya nuna kishi, ya yi abin da zai taimaka wa ƙungiyarsu domin samun nasara. Tun daga mai tsaro zuwa ɗan gaba, duk suna iya ba da gudunmawa.” Wannan magana na nuni da cewa akwai matsalar rarrabuwar kai da rashin kishi, inda wasu ’yan wasa suke iya yin ƙoƙari sosai, yayin da wasu ba su ba da cikakkiyar gudunmawa.
Gazawar Super Eagles wajen samun dama zuwa Gasar Kofin Duniya ta 2026, ba ta samo asali daga matsala guda ɗaya ba, sai daga haɗuwar matsalolin da suka haɗa da manyan matsalolin da muka zayyano a sama. Idan ƙungiyar za ta gyara waɗannan abubuwa, ta hanyar samar da ƙwararren mai horo mai ɗorewa, inganta aikin hukumar ƙwallon ƙafa, samar da tsari mai kyau a filin wasa da ƙarfafa haɗin kai a tsakanin ’yan wasa da kishin ƙasa. Haka kuma a daure a riƙa ɗauko ‘yan wasa daga dukkan sassan Najeriya, akwai yiwuwar su dawo cikin ƙarfinsu kuma su sake fafatawa a manyan gasanni nan gaba.
_______________













