Zaɓen 2027: Akwai Yiwuwar Farfesa Pantami Ya Yi Nasara – Farfesa Lawanti
Daga Bashir Yahuza Malumfashi
__________
Ƙwararren malamin jami’a kuma masanin aikin jarida, Farfesa Kabir Danladi Lawanti ya yi hasashen cewa akwai yiwuwar ɗan takarar Gwamna a Jihar Gombe a ƙarƙashin Jam’iyar PDP, Farfesa Ali Isah Pantami na iya samun nasara.
A yayin da yake bayyana hasashen nasa a shafinsa na Facebook, Malam Lawanti ya kawo hujjojin guda bakwai, domin ƙarfafa hasashen nasa, kamar haka:
Na ɗaya, Malam yana da matuƙar goyon baya saboda matsayinsa na masanin addini. Talakawa Musulmi suna matuƙar son shi.
Na biyu, mutanen Gombe suna matuƙar jin haushin Inuwa Yahaya saboda irin yadda ya gudanar da jihar a cikin shekara takwas da ya yi yana mulki. Fushin Inuwa zai iya shafar Jamilu.

Na uku, har yanzu Jamilu na jan ƙafa wajen tuntuɓar ‘yan takarar da aka kayar a zaɓen-fidda-gwani. Don haka, fushin wasu zai koma kan Jamilu.
Na huɗu, ya ce wasu suna cewa Jamilu ya jima yana cin amanarsu a siyasa. Saboda haka za su rama yanzu.
Na biyar, ɓangaren Goje shi ma yana nan. Wasu jira suke su huce haushinsu.
Na shida, Farfesa Lawanti ya ƙara da cewa, Gombe ta kasance a ƙarƙashin mulkin PDP na tsawon shekaru 16. Ko jihar tana cikin jihohin da aka ce za a bar wa Wike ya samu gwamna? Ita ma wannan maganar akwai ta.
Dalili na 7 kuma na ƙarshe, Malam Lawanti ya ce, Pantami na da ƙima (capacity).
“Wannan ra’ayina ne kawai bisa abin da nake ji daga majiyoyi masu dama. Cikin kwana kaɗan, duk wannan hasashen na iya canzawa. Amma Pantami na da damar samun nasara sosai a 2027, gaskiya.” A cewar Farfesa Kabir Danladi Lawanti, a yayin da yake ƙarƙare hasashen nasa.
Gare ku al’umma, shin yaya kuke ganin wannan takara ta Farfesa Ali Isah Pantami, akwai haske a ciki ko akasi? Ku bayyana ra’ayinku a Comment Section.
__________












