An Yi Gangamin Addu’o’in Godiya Ga Allah A Katsina
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya halarci taron addu’o’in godiya ga Maɗaukakin Sarki Allah bisa ni’imomin da Ya yi wa jihar.
An dai ware ranar 1 ga Agustan kowace shekara domin godiya ga Allah (‘Yaumush-shukr’) bisa ɗimbin ni’imomin da Allah Ya huwace wa Jihar Katsina.
Daga cikin waɗanda suka halarci taron addu’o’in na musamman har da tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari da ƙarin wasu muhimman mutane.
Taron addu’o’in godiya ga Maɗaukakin Sarki Allah ya gudana ne a Masallacin Juma’a na Othman Bn Fodio, Modoji, Katsina.
Tun da farko dai, Gwamnatin Jihar Katsina ce, a shekarar 2019 ta ƙirƙiro wannan taron addu’o’i, domin murnar haɗe masarautun Katsina da Daura, aka samar da lardi ɗaya da kuma godiya ga Allah bisa irin ni’imomin da Allah Ya yi wa jihar ta fuskoki da daban-daban.
Da yake jawabi a yayin taron, Gwamna Dikko ya ce ya zama wajibi a gode wa Allah Maɗaukakin Sarki bisa tarin ni’imomin da Ya yi wa Jihar Katsina, musamman albarkatun ƙasar noma mai inganci da kuma mutanen da ke kishin jihar.













