Daga Shanshani
A Idin bana, ina ta karakaina a tsakanin sahun masallata a Babban Birnin Tarayya Abuja, sai idona ya ƙyallaro mani kumatun tsohon Gwamnan Jihar Kano, Khadimul Islam, Abdullahi Umar Ganduje.
Ni ba Kasancewar Baban Abba a Abuja ne ya ɗauki hankalina ba, domin na daɗe da sanin cewa tuni ya ƙaurace wa Kano, saboda eh-yane-yane… kun dai gane.
Ni babban abin da ya ɗauki hankalina kuma ya cika ni da mamaki shi ne, wata MUGUWAR HARARA da na ga tsohon Gwamnan ya yi. Shi ne nake tambayar shin me ya yi zafi haka, shi ba wuta ba?
Shin wa Khadimul Islam ya hararo haka? Shin ko ya mance a sahun Sallah yake, da zai ƙullaci wani haka?













