Daga Bashir Yahuza Malumfashi
Za Mu Tunkari Matsalolin Ruwa Da Gaske A Jihar Katsina – Injiniya Tukur
Taskar Gizago ta tattauna da sabon Babban Daraktan Hukumar Ruwa ta Jihar Katsina, Injiniya Dokta Tukur Tingilin, inda ya bayyana irin babban ƙalubale da matsalolin da ya iske a hukumar da kuma tsare-tsare da matakan da zai ɗauka domin ganin ya samu nasarar shawo kansu:
Allah Ya ba ka ikon zama Babban Darakta na Hukumar Ruwa ta Jihar Katsina, yaya ka iske hukumar bayan ka shiga ofis ka kama aiki?
A matsayina na sabon Babban Darakta na Hukumar Samar Da Ruwa ta Jihar Katsina, na tarar da matsaloli katutu da yawa da suka cunkushe wannan ma’aikata, ta yadda ta koma kamar ma ba ta da wani amfani a faɗin jihar.
Waɗanne irin matsaloli ne ka samu?
Na samu matsalar da ta shafi sinadaran tsarkake ruwa. Akwai kuma rashin issssar wuta mai ƙarfi da ta ke ba manyan tashoshin ruwanmu guda biyar na Jihar Katsina, watau, Ajiwa, Zobe, Funtua, Malumfashi da Jibia da sauran tasoshi, kamar Sabke a Daura da sauransu. To wannan matsala ita ce ta fi ci mana tuwo a ƙwarya. Ita ce ke sa Gwamnatin Jihar Katsina take kashe maƙudan kuɗaɗe domin ganin ta tace ruwan da za a ba al’umma, kasancewar ganin man gas ya yi tsada. Ga shi ita kanta wutar, za ka tarar wani lokaci akwai ta amma ƙarfinta ba ya kai wa inda injinan za su iya ɗauka. Wani lokaci kuma sai ƙarfin nata ya fi adadin da su injinan suke buƙata, kasancewar an yi su don su zama masu ɗaukar wutar kai tsaye (automatic), sai su kashe kansu su ƙi aiki. Kan haka sai ka ga akwai wutar amma ba ta da amfani.
Akwai matsalar wasu wurare inda aka samu ɓatagari suka lalata a Sabke, a Daura ke nan. Da kuma ɓarnar da ruwa da iska ta yi a wasu wuraren kuma ba a gyara ba.
Ta ɓangaren ma’aikata kuma fa, ko akwai abin da ka gano?
Ƙwarai kuwa, akwai ƙarancin ma’aikata da kuma batun horo na ma’aikatan da ke akwai, domin ma’aikatan wucingadi sun ninninka na dindindin. Idan an lura, ma’aikacin wucingadi ba lallai ne ya yi maka abin da kake bukata ba, kasancewar
ya san cewa shi ba cikakken ma’aikaci ba ne.
Waɗannan su ne matsalolin da muka samu amma in sha Allahu za mu tunkare su ɗaya bayan ɗaya domin magance su.
To, ta yaya za ka tunkari magance waɗannan matsaloli, a matsayinka na Shugaba a wannan hukuma?
Misalin matsalar tsadar man gas, ina shigowa ofis, mai girma Gwamna ya umurci mataimakinsa ya ba mu damar tunkarar matsalarmu da ta shafi man na gas, cewa mu tunkari sayen shi kai tsaye. Game da maganar wuta kuwa sai muka zauna da Mataimakin Shugaban Ma’aikata na gidan gwamnati, tare da Hukumar Wutar Lantarki ta Kano, wacce ita ce ke ba mu wutar nan, aka tattauna, aka kafa kwamiti. Don haka daga makon nan za mu fara zagayawa, domin tabbatar cewa mun gano matsalar, an warware ta da gaggawa, domin a taimaki gwamnati wajen rage maƙudan kuɗin da take kashewa wajen sayen man gas.
Ta ɓangaren ma’aikata kuwa, za mu tantance na wucingadi, domin ba gwamna shawara, a duba su domin ganin sun zama ma’aikata na dindindin. Su kuma ma’aikatan da muke da su, za mu ɓullo da hanya ta gaggawa domin ganin cewa mun sake ba su horo domin su samu ƙwarewa da damar yin gogayya wajen aiki na zamani.
Ta ɓangaren al’ummar Jihar Katsina, ko wane haɗin kai kake buƙata daga gare su?
Daga ɓangaren al’ummar Jihar Katsina kuwa, haɗin kai da muke nema daga gare su shi ne, su sani cewa ita wannan ma’aikata ta dogara ne daga kuɗaɗen da suke biyan ta, a dalilin ruwan da suka sha, domin biyan albashi da gudanar da harkokinta na yau da kullum. Don haka muna kira ga jama’a da su yi la’akari da canjin da aka samu, yadda ake kawo ruwa a yanzu haka. Don haka su maida wa gwamnati karimcin da ta yi masu, su riƙa biyan kuɗin ruwa a kan lokaci. Abu na biyu kuma shi ne, ruwan nan in Allah Ya yarda zai inganta, a ci gaba da bayar da shi, kamar yadda mutane suke ganin shi a kai-a kai. Ina kira ga waɗanda ba su da kan famfo da su yi azama su je ofishin hukumar ruwa a inda suke domin yin rijista, domin su ma su riƙa amfana daga wannan tagomashi na Gwamnatin Malam Dikko Raɗɗa dangane da ruwan sha.
Game da kayan hukumar kuma, waɗanda ake lalatawa da ɓarnatawa a wasu wurare, muna kira ga al’ummar Jihar Katsina da su taimaki wannan hukuma, domin tabbatar da cewa, duk inda aka ga irin wannan ɓarna ko kan famfo ya karye yana zubar da ruwa, su yi gaggawar sanar da ita. Inda kan fanfunan suke tsaye kuwa, a taimaka a sa ido a hana yara da suke ɓarna da kuma ɓarayin fanfunan nan, ‘yan bolabola ke nan, domin kuwa dukkan waɗannan abubuwa na su ne kuma domin jin daɗin su ne gwamnati ta samar da su. Ke nan sai mu ma mun maida hankali wajen kare su. Muna ba da albishir cewa in sha Allahu wannan ci gaba zai ɗore domin amfanin kowa.














Za Mu Tunkari Matsalolin Ruwa Da Gaske A Jihar Katsina – Injiniya Tukur – Taskar Gizago
apwwkbqtqoj
[url=http://www.g62mvgb5a6xo7p457z2n067c493spga3s.org/]upwwkbqtqoj[/url]
pwwkbqtqoj http://www.g62mvgb5a6xo7p457z2n067c493spga3s.org/