TSOKACINMU NA YAU (04)
Yau Talata, 04-Ramadan-1446, Hijirar Manzon Allah (saw), wacce ta yi daidai da 04-Maris-2025 Miladiyya.
Ga tsokacinmu na yau:
“Ya ku ‘yan uwa, Allah Ya umurce mu da mu kasance masu haƙuri kuma Ya ce yana tare da masu haƙuri. Haƙuri shi ne juriya da duk wani abu da zai sosai mana rai, ko saboda rashi ko akasin sa.
Ke nan, dai haƙuri wani ƙalubale ne a rayuwarmu. Shi ne tubalin kai wa ga kowace irin nasara.
Masu iya magana sun ce, mai haƙuri shi ke dafa dutse, har ya sha romonsa. Haka kuma sun ce, abin da duk haƙuri bai ba ka ba, to rashin sa ba zai ba ka ba.
Ya Allah, Ka ƙara mana haƙuri da juriyar fuskantar kowane ƙalubale na rayuwa kuma Ka ba mu sakamakon da Kake ba masu haƙuri, duniya da lahira, Amin.”
Allah sa mu dace, Amin.
Mu wuni lafiya.
Naku,
Bashir Yahuza Malumfashi,
Editan Mujallar Taskar Gizago.












