Daga Bashir Yahuza Malumfashi


A Harkar Rubutu: Na Fi Fuskantar Matsala Daga Mata – Uwa Idris
~~~~~~~
Sunanta A’isha Giɗaɗo Idris amma an fi sanin ta da laƙanin Hajiya Uwa. Marubuciya ce mai hazaƙa. Ta rubuta littattafai da dama a cikin Ingilishi da Hausa. A yanzu kuwa sunanta ya buga tambura a soshalmediya, inda take rubuce-rubuce da suka shafi zamantakewar aure da soyayya tsakanin maza da mata. Wasu na yi mata kirari da Lauyar Maza. Domin sanin cikakken tarihi da gwagwarmayar da take sha a fagen rubutu, Taskar Gizago ta tattauna da ita:
~~~~~~~
TG: Kina ɗaya daga cikin marubuta na dauri, ko za ki gaya mana tarihinki a taƙaice?
Hajiya Uwa: Ni sunana A’ishatu Giɗaɗo Idris, ana kuma kira na da laƙanin Uwa.
An haife ni ne a garin Zariya, watan Yuli, 1960.
Ban yi nisan karatu ba, yadda mutane da yawa suke zato. Na yi makarantar firamare a wurare da yawa. Amma na fi daɗewa a makarantar kwana ta Kakuri.
TG: Tun yaushe kika fara rubutu kuma mene ne ya ja ra’ayinki ga harkar rubuce-rubuce?
Uwa Idris: Na fara rubutu a 1991 ne, a lokacin da nake fuskantar ƙalubale game da zamana da mijina, a matsayin matarsa ta farko a lokacin. A lokacin ne na rubuta littafina na farko, mai taken “Rabiat” wanda na Turanci ne.
TG: Ya zuwa yanzu, littattafai nawa kika rubuta? Guda nawa aka buga a littafin takarda kuma nawa kika buga a intanet?
Uwa Idris: Na rubuta littattafai tara. Na Hausa guda biyar, na Turanci guda huɗu. Kuma duk an buga su a takarda.
A intanet kuwa, na saka na Turanci duka a wattpad.com Sauran kuwa na Hausa ne, ban riga na saka ba tukuna.
TG: Waɗanne irin matsaloli kike fuskanta a matsayinki na marubuciya, musamman ma a soshalmidiya?
Uwa Idris: Tabbas matsalolin da nake fuskanta a matsayina na marubuciya a soshalmidiya suna da ɗan yawa, musamman matsalolin sun fi danganta da maganar mata da suke rashin sanin muhimmancin zamantakewar aure mai kyau.
Wasu matan da yawa, sukan ƙi na’am da ra’ayina tare da tunanin ina yawan ba su laifi a abubuwan da ke faruwa tsakaninsu da mazansu.
Wani lokacin kuma, ina samun waɗanda suke mani maganganu cikin zargi, ɓacin rai da adawa.
Wasu kuma su yi mani mummunar fahimta, tare da ganin laifina a rubuce-rubucena da suka danganci aure. Da yawan mutane masu bibiya ta sun sha nuna cewar sun gaji da ina zama lauyar maza.
TG: Tun daga fara rubutu, waɗanne irin nasarori kika samu ko kuma akasin su?
Uwa Idris: Tun da na fara rubutu, na samu nasorori irin na zama sananniya a al’umma. Kuma ana yawan kallo na a matsayin wadda a hankali za ta kawo canji.
TG: A harkar rubuce-rubuce, waɗanne marubuta ne gwanayenki, da kike koyi da rubutunsu?
Uwa Idris: A marubuta ina koyi da Amina Abdulmaleek, Bashir Yahuza Mulumfashi, Alawiyya Wada Isa da Ibrahim Sheme.
TG: An daɗe ba a ji ɗuriyarki da sabon littafi ba, shin me ya faru, ko kin daina buga littafi ne?
Uwa Idris: Allah Sarki! Ban daina ba. Abin da yake faruwa shi ne, na ɗan shagala ne da rubutu a soshalmidiya. Sai nake ganin bari in ɗan jira sai na tuno da yanayin abin da nake son magana a kai. Amma in sha Allah bayan na gama littafin da ke gabana yanzu, mai taken “A Birkice Ra’ayin Yake” wanda na tarihin rayuwata ne, zan yi rubutu a kan zamani.
TG: Wasu marubuta sun koma rubutun fim, ko ke ma kina da shirin hak?
Uwa Idris: Gaskiya zan so in zama mai rubuta script. Amma ban san yadda za a fara ba.
TG: Mene ne babban burinki dangane da rubutu?
Uwa Idris: Babban burina game da rubutu shi ne, ya zamana rubutu yana karɓuwa, kuma ya zama mara yawa sosai. A wannan zamanin babu abin da ba a so da yawa irin rubutu. Ina fatan a samu marubuta masu koyi da cewar duk abubuwan da yake faruwa a wannan zamanin, ba ƙarya ba ne, kuma su jure da bayanin cewa shi zamani ikon Allah ne.
TG: Ko kina da wani kira ga gwamnati da marubuta ‘yan uwanki da kuma al’umma masu karanta littattafanki?
Uwa Idris: Ina kira ga gwamnati da ta kafa hukuma mai kyau ta buga littattafai a kowace jiha, domin ta riƙa tallafa wa marasa ƙarfi, waɗanda ba su iya buga littattafansu da kansu. Sannan zan yi fatan marubuta su riƙa rubutu a kan canjin lokaci da ke ɓata wa matasanmu saiti.












