D

aga Bashir Yahuza Malumfashi
Shugaba Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya karrama wasu fitattun mutane daga sassa daban-daban na Najeriya, ciki har da wasu shahararru daga Arewa, inda ya sanya sunayensu a filayen jirgin sama 15 na sassan ƙasar nan.
Shahararrun ‘yan Arewa da aka karrama sun haɗa da Mujaddadi Shehu Usmanu Ɗanfodiyo, wanda aka sanya wa Filin Jirgin Sama na Nassarawa sunansa. Sai Filin Jirgin Kaduna, wanda aka sanya wa sunan Hassan Usman Katsina da na Maiduguri, wanda aka sanya wa tsohon Shugaban Ƙasa Janar Mumammadu Buhari.
Sauran su ne, Filin Jirgin Sama na Makurdi, aka sanya wa Joseph Sarwuan Tarka da na Dutse, wanda aka sanya wa Muhammad Nuhu Sanusi. Sai kuma Filin Jirgin Sama
na Gombe, wanda aka sanya wa sunan marigayi Birgediya-Janar Zakari Maimalari. Akwai kuma Filin Jirgin Sama na Ilorin, wanda aka sanya wa marigayi Janar Tunde Idiagbon.
Fitaccen marubucin littattafan Hausa, marigayi Malam Abubakar Imam, shi ma ba a bar shi baya ba, domin kuwa an sanya wa Filin Jirgin Sama na Minna sunansa. Sai kuma Filin Jirgin Sama na Yola, wanda aka sa sunan Lamido Aliyu Mustapha.
Sauran ‘yan ƙasa da aka karrama sun haɗa da Olumuyiwa Bernard Aliu (Filin Jirgin Sama na Akure), Oba Akenzua II (Filin Jirgin Sama na Benin) da Chuba Wilberforce Okadigbo (Filin Jirgin Sama na Ebonyi) da Samuel Ladoke Akintola (Filin Jirgin Sama na Ibadan) da Alfred Diete Spiff (Filin Jirgin Sama na Osubi). Sai kuma Filin Jirgin Sama na Fatakwal, wanda aka sanya wa sunan Obafemi Jeremiah Awolowo.














Wannan labarin maimaici ne a kan abin da Buhari ya yi daf da zai sauka daga karagar mulki. Sai dai a ce shugaba Tinubu ya daɗa tabbatar da wannan abin da Buhari ya yi kafin ya sauka. Illa iyaka.