Mataimakin babban limamin Babban Masallacin Abuja, Sheikh, Farfesa Ibrahim Maƙari ya bayyana cewa Malaminsa yana sauke Alƙur’ani mai cikin ƙasa da rabin awa.
Fitaccen malamin ya faɗi haka ne a cikin wani faifan bidiyo, inda yake magana kan irin baiwa da karamar da Allah Ya ba Malaminsa. Duk da cewa bai ambata sunan malamin nasa ba, amma ya ce yana ɗaya daga cikin mafi kusa da shi.
Malamin ya nuna cewa wasu za su yi mamaki a ce wani ya sauke Alƙur’ani a ƙasa da minti 30, to amma a cewarsa, wannan ba abin mamaki ba ne ga wanda Allah Ya hore ma wa.














Lokaci a gurinka bashine lokaci a wurin kowa ba, idan da zakayi muámala da masana koda acikin turawa zaka samu wanda zai karanta littafi shafika masu yawan gaske, a inda zaka ga akan dauke mafiya yawan mutane shekara ko shekaru.
Nasan duk mai qoqarin saka shakku ga wani Alámarin da shi lokacinsa bai kai ba, zai iya saka shakku ga wannan Hadithin na Tahajjud: Da Awf ibn Malik ya shaida faruwarsa akan Sallar ManzonAllah SallalLahu AlaiHi wa AaliHi wa Sallam a Sallar Dare:
عَنْ عَوْفِ بْنِ مَالِكٍ الْأَشْجَعِيِّ قَالَ قُمْتُ مَعَ رَسُولِ اللَّهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ لَيْلَةً فَقَامَ فَقَرَأَ سُورَةَ الْبَقَرَةِ لَا يَمُرُّ بِآيَةِ رَحْمَةٍ إِلَّا وَقَفَ فَسَأَلَ وَلَا يَمُرُّ بِآيَةِ عَذَابٍ إِلَّا وَقَفَ فَتَعَوَّذَ قَالَ ثُمَّ رَكَعَ بِقَدْرِ قِيَامِهِ يَقُولُ فِي رُكُوعِهِ سُبْحَانَ ذِي الْجَبَرُوتِ وَالْمَلَكُوتِ وَالْكِبْرِيَاءِ وَالْعَظَمَةِ ثُمَّ سَجَدَ بِقَدْرِ قِيَامِهِ ثُمَّ قَالَ فِي سُجُودِهِ مِثْلَ ذَلِكَ ثُمَّ قَامَ فَقَرَأَ بِآلِ عِمْرَانَ ثُمَّ قَرَأَ سُورَةً سُورَةً
873 سنن أبي داود باب تفريع أبواب الركوع والسجود باب ما يقول الرجل في ركوعه وسجوده
3/413 المحدث النووي خلاصة حكم المحدث إسناده صحيح في المجموع للنووي
Muna yaba aikin wannan jarida bisa ingatattun labaran dasuke kawo mana.
Ma sha Allah! Muna godiya sosai Malam. Kuma muna rokon a ci gaba da taya mu da addu’a domin mu samu karfin ci gaba da yardar Allah.