Daga Bashir Yahuza Malumfashi
A karon farko, Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya yi magana game da tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Godwin Emefiele, wanda ya dakatar a kwanakin baya kuma Hukumar DSS ke binciken al’amuransa.
Shugaban na Najeriya ya ɓara ne a yayin ganawa ta musamman da ‘yan Najeriya mazauna ƙasar Faransa da maƙwabtanta a Nahiyar Turai. Ya ce a zamanin da yake shugabantar bankin, ya lalata al’amura da tsarin gudanar da dukiyar Najeriya.
A cewarsa, ‘yan Najeriya da dama da suke zaune a ƙasashen waje sun fuskanci matsaloli da suka shafi aika kuɗi ga ‘yan uwansu saboda yadda aka riƙa ninka masu kuɗin la’ada. Sai dai shugaban ya ce a mulkinsa, waɗannan matsaloli za su zama tarihi.
“Tsarin gudanarwa da tafiyar da al’amuran kuɗi ya ruɓe. Mutane ‘yan ƙalilan ne ke samun manyan kuɗaɗe daga dukiyarmu, sannan ku da kanku kuka tsayar da aika wa iyayenku da ‘yan uwanku da marayu da zawarawa mabuƙata kuɗi. Amma dai ina ba ku tabbacin cewa, wannan matsala za ta zama tarihi a yanzu.
“A halin yanzu mutumin nan (Emefiele) yana hannun hukumomi, za su yi abin da ya dace. Za su tantance al’amura da juna.” In ji Shugaban Ƙasa Tinubu.













