An Kama Wasu Mata Da Ke Safarar Makamai Zuwa Katsina
Daga Muhammad Aminu Kabir
~~~~~~~
An kama wasu mata guda biyu a mabambantan lokuta, suna ɗauke da tarin alburusan da suka yo safararsu daga jihohin Taraba da Bauchi.
Ɗaya matar (an sakaya sunanta), an kama ta ne a tashar mota da ke garin Jibiya, tana ɗauke da albarusan bindiga sama da 400.
Kamar yadda bayanai suka nuna, tun daga Jihar Taraba take ɗauke da wannan kayan laifi amma ba a kama ta ba sai a cikin tashar mota, bayan da jama’ar gari suka tsananta da ita suka fara binciken ta.
Mace ta biyu, wacce ke cikin hijabi (an sakaya sunanta), ita ma jami’an tsaro suka cafke ta a Jihar Katsina. Ta taso tun daga Jihar Bauchi, inda ta yo safarar harsasun bingida zuwa Katsina.
Jami’an tsaro a Jihar Katsina suna kan tsaurara bincike a kan matan biyu.
“Da haka ake shawartar al’umma da su saka ido sosai ga bakin mutane a yankunansu. Duk wanda ba a aminta da yanayinsa ba, a kai koke ga jami’an tsaro domin su bincika,” inji wani jami’in tsaro, yayin da yake tsokaci game da al’amarin tsaro a Jihar Katsina.
~~~~~~~














Maashaa Allah. Allah ya kara tona Asirin ire-irensu, da masu daure masu gindi
Amin Amin Ya Allah. Muna godiya da bibiyar mujallar Taskar Gizago.