Daga Wakilinmu
Jami’an Tsaro a Nijar sun damƙe wani Malamin Musulunci mai suna Gausi Almustapha bisa zargin shi da wuce gona da iri, inda ya auri mata saba’in 75.
Malamin wanda yake zaune a ƙauyen Tudun Faira a yankin Dogon-Dutse na Jihar Dosso, ya yi ƙaurin suna, inda yake ikirarin cewa shi ne Mahadi, wanda zai zo a ƙarshen duniya.
Haka kuma hukumomin na tsaro sun zarge shi da laifin bautar da mabiyansa, inda yake sanya su aikin noma a manyan gonakinsa. Yana kuma aure ‘ya’yansu ba tare da bin tsarin Shari’ar Musulunci ba ta hanyar noman manyan gonakinsa tare da aura masa ƴaƴansu mata.
A halin da ake ciki dai, malamin yana tsare a gidan maza, inda ake shirin yanke masa hukunci.














Allah ya tsaremana Gwamnanmu Allah ya bashi ikon auyin da Allah ya doramashi
Amin Ya Rahman!