Daga Bashir Yahuza Malumfashi
~~~~~~~
A yau ba sai gobe ba, idan dai ana maganar rubutattun wakokin hikima na Hausa, sunan Malam Abubakar Alkantamawy ya buga tambura. Wane ne shi kuma tun yaushe ya fara wannan harka ta waƙa? Mene ne babban burinsa a rayuwa? Me ya sanya ba ya saka kiɗan zamani a w

aƙoƙinsa domin sajewa da zamani? Waɗannan da ma wasu tambayoyi ne TASKAR GIZAGO ta yi masa, inda shi kuma ya amsa su cikin hikima. Ga yadda tattaunawar ta gudana:
~~~~~~~
TG: Kasancewar wannan ne karon farko ganawa da Taskar Gizago, ko za ka fara gabatar mana da tarihinka a taƙaice?
ALKANTAMAWY: To, alhamdu llilah. Wassalamu ala Rasulillah. Bayan haka, da farko sunana Abubakar Ibrahim Kantama (Alkantamawy). An haife ni a ƙauyenmu Kantama cikin Ƙaramar Hukumar Minjibir a Jihar Kano. Na fara karatun Alƙur’ani a gidanmu, kafin daga baya na fara fita ƙarin karatun addini a Jihar Gombe.
A ɓangaren karatun zamani kuma, na yi firamare da sakandare da Difiloma. A ƙarshe kuma na kammala Digiri a harshen Larabci a shekarar 2012 a ƙasar Sudan. Kuma ni malamin makaranta ne, kuma ina ayyukan yaɗa da’awar addinin Musulunci.
Ɓangaren iyali kuma ina da iyali har da yara maza da mata.
TG: Tun yaushe ka fara rubutawa da rera waƙa kuma me ya ɗauki hankalinka zuwa ga wannan harka ta waƙa?
ALKANTAMAWY: Na fara rubuta waƙoƙin faɗakarwa da harshen Hausa tun a shekarar 1998. Haka kuma wasu da dama nakan rera su tun a zamanin kaset na rediyo har zuwa zamanin sarrafawa da komfuta. Wasu kuma a rubuce kawai suke ba a rera su ba. Kuma a gaskiya tun farko sha’awa da son faɗakarwa ta wannan salo na waƙa, su suka sanya ni shiga cikin wannan fage mai albarka.
TG: Ya zuwa yanzu ko waƙoƙi nawa ka rubuta?
ALKANTAMAWY: A gaskiya wannan tambayar tambaya kullum har tsoro nake a yi min ita! Domin gaskiya amsarta takan min wahala ne, domin gaskiya tsakanin dogaye da gajerun ƙasidu, waɗanda aka rera da waɗanda ba a rera ba; gaskiya yawansu yana da yawa. Domin ko a wannan shekarar kaɗai za a iya samun aƙalla sama da hamsin.
TG: Ko me ya sa ka tsaya ga salon rubutattar waƙa da rerawa ba tare da kiɗa ba, kamar yadda wasu mawaƙa suke yi a zamanance?
ALKANTAMAWY: To, a haƙiƙa na zaɓi tsayawa ga tsarin rubutacciyar waƙa saboda ita ta fi burge ni. Haka kuma na rinjaya ga wannan salon na rerawa, ba tare da kiɗa ba, tun kusan shekarar 2008 zuwa yanzu. Za ka tarar kashi 95 cikin 100 na yi su ne babu kiɗa. Duk da cewa wasu daga cikin malamai suna nuna halaccin waƙa da kiɗan, matuƙar ba haram ake yabo ko tallatawa ba. To amma bisa la’akari da ƙasidun nawa, mafi yawa na wa’azi ne, waɗanda babba da yaro suna buƙatuwa zuwa jin saƙon ko a cikin masallaci ne. Don haka sai na fifita yin su a haka ɗin don saƙon ya game kowa.
TG: Kwanan nan aka ƙaddamar da Kundin Waƙoƙinka a Katsina. Shin ko za ka ba mu labarin yadda al’amarin ya faro?
ALKANTAMAWY: Lallai haka batun yake. An ƙaddamar da Diwanin wasu daga cikin ƙasiduna, mai shafi wajen ɗari uku da sittin da shida (366) kuma ya ƙunshi tarihina da tarihin harkar waƙoƙin nawa, sannan da cikakkun ƙasidu har guda ɗari ɗaya da bakwai (107).
Yadda batun ya taso kuwa shi ne, shi marubucin littafin, Malam Adam Mainasara Katsina, yana cikin aikin nazarin ƙasidun nawa a karatunsa na Digiri na uku a Jami’ar Bayero Kano (B.U.K), to a lokacin da yake zuwa muna tattaunawa sai ya lura babu wani dunƙulallen littafi da ya ƙunshi ko da kaɗan daga ƙasidu, duk ƙasidar da ya nema sai dai in lalubo takardun a adakata, ko daga memory, ko tsohon kaset, wasu ma sai dai a lalubo su a shafina na Facebook. Wannan ya sa malamin ya lashi takobin sai ya tattara wasu ƙasidun a kundi, duk da wancan aiki da yake ciki na karatunsa. To da taimakon Allah kuwa sai hakan ta tabbata kuma wani ƙarin ci gaba, sai Jami’ar Alƙalam Katsina, wadda yake koyarwa a cikinta, ta ɗauki gabarar jagorantar bikin ƙaddamar da kundin, ƙarƙashin jagororin shugabanta, Mai girma Farfesa Nasiru Musa Yawuri; a ranar Asabar (13-5-2023). Kuma masoya daga sassa da dama sun samu halartar taron, an yi komai cikin nasara, Alhamdu llilah.
TG: Wace gamsuwa ko fa’ida ka samu daga wanann kundi?
ALKANTAMAWY: Alhamdu llilahi. A gaskiya tun daga farkon aikin rubuta kundin har zuwa ƙaddamar da shi, na ƙara gamsuwa cewa lallai akwai ɗimbin masoya masu kishin wannan harka, kuma suke da sha’awar taimaka wa ci gabanta ta kowacce fuska. Tabbas duk wanda ya halarci taron zai tabbatar da haka. Sannan kuma wannan ya tabbatar da cewa ashe saƙon namu ya kai inda ba a zato, tun da har manyan masana daga manyan jami’o’i, Kai har da shugabannin jami’o’n za su bai wa wannan sha’ani kyakkawar kulawa kamar haka, to ko shakka babu Allah Ya sanya albarka cikin lamarin. Allah ya saka wa kowa da alheri.
TG: A wannan harka ta waƙa, wane abu na baƙin ciki ya taɓa samun ka, wanda ba za ka mance da shi ba?
ALKANTAMAWY: A hakikanin gaskiya tun da na fara wannan hidima babu wani taƙamaiman babban ɓacin rai da ya kai ga ya zauna min a zuciya, wanda har ba zan manta shi ba. Domin kasancewar ƙasidun nawa ba sa taɓa mutuncin kowa, wannan ya sa babu wani abu na cin mutuncina da aka yi, ko wata barazana gare ni. Alhamdu lillahi. Sai dai ‘yan ƙananan ƙalubale da na ɗan fuskanta aƙalla guda biyu:
1- Tun a farkon marra, an samu wasu da suka riƙa ƙyamatar ganin ina layin almajirci kuma na shiga wani abu da su a ganin su suna jin tsoron kada in koma maroƙi ko mai haifar da cece-kuce. Wannan har sai da ya jawo mahaifina da malamaina suka yi yunƙurin hana ni ci gaba da waƙa, amma daga ƙarshe sun gindaya min sharuɗɗa, suka bar ni na ci gaba.
2- Kasancewar ƙasidun nawa na wa’azi ne, to sai ya zamo babu wasu tabbatattun hanyoyin samar da ‘yan kuɗaɗen da za mu ji daɗin gudanar da ayyukan rerawa da yaɗawa, sai ɗan abin da na samar da gumina, ko kuma wasu suka iya tunanin tallafawa, kodayake hakan yana da ƙaranci; sai ‘yan ƙalilan cikin bayin Allah, tun da ba a rasa nono a ruga.
TG: Kuma a wannan harka, wane abin alheri da farin ciki ya taɓa samun ka, wanda ba za ka iya mance shi ba?
ALKANTAMAWY: A gaskiya tun da na fara zuwa yau, abin alherin da ba zan taɓa mantawa ba, babu kamar zuwa aikin Hajji da na yi a shekarar 2017, inda tafiyar ta zo min ba zato ba tsammani, Kuma cikin ƙurarren lokaci amma Allah Ya tabbatar da tafiyar ƙarƙashin sahalewar Shugaban Hukumar Alhazai ta Ƙasa na lokacin, Barista Abdullahi Mukhtar (Allah saka masa da gidan Aljanna). Sannan kuma sai tattara kundin can da ƙaddamar da shi.
TG: Mene ne babban burinka a nan gaba game da harkar waƙa?
ALKANTAMAWY: Babban burina a wannan harkar shi ne saƙon nawa ya shafi kowanne fannin addini da rayuwa, kuma ya zamo ya riski kowanne mai fahimtar Hausa a duk matakin da yake, ba tare da taɓa mutuncin kowa ba. Ƙarshe kuma hakan ya zamo sanadin shiga Aljanna gare mu gaba ɗaya.
TG: Daga ƙarshe, shin ko ka taɓa yin nadamar zama mawaƙi a rayuwarka?
ALKANTAMAWY: Ban taɓa nadama ba ko sau ɗaya, kuma ban ji kamar zan yi nadamar hakan a nan gaba ba in sha Allahu. A ƙarshe ina jaddada godiya ga Taskar Gizago mai albarka da dukkan masu gudanar da ita. Ubangiji Allah Ya ƙaro haske da albarka, Ya saka muku da mafificin alheri. Na gode!













