Daga Bashir Yahuza Malumfashi
Mai girma Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Ibrahim Namadi, ya naɗa ƙwararren ɗan jarida, marubuci kuma mai sharhi kan al’amuran yau da kullum, Malam Muhammed Hamisu Gumel, a muƙamin Sakataren Watsa Labarai, jim kaɗan da rantsar da shi a kujerar mulki.
Ko wane ne Hamisu Gumel? An haifi ƙwararren ɗan jaridar ne a ranar 15 ga watan Agusta, 1976, a Ƙaramar Hukumar Gumel, Jihar Jigawa. Ya yi karatu har zuwa matakin Jami’a, inda ya samu shaidar digiri a fannin aikin jarida a Jami’ar Bayero Kano.
A rayuwarsa ta neman ilimi, ya halarci kwasakwasai a fannonin aikin jarida, harkar hulɗa da jama’a da kuma ƙwarewa a harkar jin ƙai da kare haƙƙin ɗan Adam a Najeriya da ƙasashen waje daban-daban. Kan haka ne ya samu cancantar zama mamba a ƙungiyoyin ƙwararrun ma’aikata da suka haɗa da Ƙungiyar Ƙwararrun Jami’an Hulɗa da Jama’a ta Najeriya (NIPR) da Ƙungiyar Ƙwararrun Masu Ba Da Agajin Jin Ƙai (PHAP), Ƙungiyar Masu Ba Da Hidima A Fannin Harsuna ta Najeriya (LASPAN) da kuma Ƙungiyar Masu Fassara Yaruka ta Duniya.
A fannin aiki kuwa, Malam Hamisu ya yi aiki a wurare daban-daban, waɗanda suka haɗa da, Hukumar Fiscal Responsibility Commission, Abuja daga 2011 zuwa bana, inda ya riƙe muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’in Watsa Labarai. Ya yi aiki a Majalisar Tarayya Abuja, a matsayin Jami’i mai taimaka wa Shugaban Majalisar Wakilai ta Tarayya, kan abin da ya shafi Kwamitin Kula da ‘Yan Gudun Hijira. Ya taɓa aiki a Hukumar Watsa Labarai ta Ƙasa daga 2002 zuwa 2011 a matsayin Babban Jami’in Kula da Tantancewa a Shiyyar Kaduna, sannan aka matsa da shi zuwa Jihar Katsina a matsayin mai kula da jihar baki ɗaya.
Gumel ya taɓa yin aiki da gidan jaridar Crystal International Newsmagazine, a shekarar 2001 zuwa 2002, a matsayin ɗan rahoto da kuma jami’in bin ƙwaƙƙwafi. Ya taɓa zama Editan Mujallar Fim a Kaduna, a shekarar 2001. Ya taɓa yin aiki a bankin Tropical Commercial Bank, a shekarar 2000 zuwa 2001, inda ya yi hidimar ƙasa (NYSC). Haka kuma ya taɓa yin aiki a kamfanin jaridar The Shield Weekly/Garkuwa Newspapers, Kano a shekarar 2000, a matsayin ɗan rahoto.
A matsayinsa na ƙwararren marubuci kuwa, Malam Hamisu ya rubuta littattafai da dama cikin harsunan Ingilishi da Hausa, cikinsu har da littafi Mai taken Sadauki Umar, wanda ya zayyano hikiyar Sahabin Annabi Muhammadu (saw), Umar bin Kaɗɗab (ra).
Kasancewar shi mutum mai haƙuri da juriya, gami kuma da iya mu’amala da jama’a, wannan muƙami da Gwamnan Jihar Jigawa ya ba shi, babu shakka ya dace. Hasali ma za a iya cewa a sargaye ƙwarya a daidai ragayarta.
Muna yi masa fatan alheri da addu’ar Allah Ya taya riƙo, amin.












