Daga Bashir Yahuza Malumfashi
Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya sauke dukkan shugabannin rundunonin tsaro na Najeriya kuma ya sanar da sunayen wadanda za su maye gurabensu, ba tare da jinkiri ba.
A wata takardar sanarwa da ta fito daga Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, ɗauke da sa hannun Babban Daraktan Watsa Labarai, Mista Willie Bassey, ta bayyana sunayen sababbin shugabannin rundunonin tsaron da masu ba Shugaban Ƙasa shawara na musamman kamar haka:
Malam Nuhu Ribadu (Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro), Manjo-Janar C.G Musa (Shugaban Rundunar Tsaro), Manjo-Janar T. A Lagbaja (Shugaban Rundunar Sojojin Najeriya), Riya-Adimiral E. A Ogalla (Shugaban Rundunar Sojojin Ruwa ta Najeriya) da Eya-Bayis-Mashal H.B Abubakar (Shugaban Rundunar Sojojin Sama ta Najeriya). Haka kuma an naɗa DIG Kayode Egbetokun, a matsayin Babban Sufeto-Janar na ‘Yan Sandan Najeriya (na riƙo).
A ɓangaren Kwatsam kuwa, Shugaban Ƙasa ya amince da naɗin Adeniyi Bashir Adewale a matsayin Shugaban Hukumar Kwastam na riƙo.













