YADDA SHARA TA MAMAYE BIRNIN KATSINA!
Daga Yazid Nasudan
~~~~~~~
Birnin Katsina kamin yanzu yana cikin birane mafiya tsafta a duk fadin Arewacin Najeriya tunda aka kafa hukumar SEPA a zamanin tsohon Gwamnan Jihar katsina Mal Umaru Musa Yar’adua yanayin tsabtar Birnin ya sauya inda a kan ga Jami’an hukumar suna ta sintiri da motocin su suna kwashe duk wata shara da aka tara a cikin unguwannin birnin, baya ga wasu ma’aikatan hukumar da suke share titunan Birnin duk safiyar Allah Ta’ala. Haka Kuma duk shekara lokacin bazara Jami’an hukumar kan bi ko Ina a fadin Birnin katsina su bude magudanan ruwa su kwashe duk wata shara ko dattin da aka zuba ciki.

A baya bayan nan lokacin shugaban hukumar na karshe Alhaji Isah Saidu Barda hukumar ta kai kololuwar matsayi na cigaba inda bayan tsabatace Birnin katsina har ta rika gudanar da wasu ayyukan da suka hada da sarrafa sharar domin samar da taki da ta kan sayar ga manoma, ga Kuma shaguna mallakin hukumar da ta gina a wuraren daban daban cikin Birnin katsina kamar a Gwangwan ta gina kasuwar zamani da Kuma wasu a kusa rawun din liyafa. Sai dai duka wancan cigaban da Hukumar ta fara samu wanda ake ganin da ya dore nan gaba zai iya kai hukumar ga matakin da zata iya dogara da kanta, alamu na nuna cewa an baro bide baya, domin a halin da ake ciki ko sharar ma hukumar bata iya kwashewa bare Kuma a sa ran wani abu daban.
Wani abin takaici yanzu hukumar bata iya kwashe shara har sai mutane sun yi koke koke a kan hakan, Kuma idan za’a kwashe sharar har sai an gayyato Yan jarida suna dauka wai ga hukumar SEPA na kwashe shara Kai jama’a !!! Da wama ya san lokacinda suke kwasheta ? Ba sai dai ka ga babu ita ba kawai.
A halin da ake ciki yanzu gaba daya duk wani wurin da ake tara shara a Birnin katsina cike yake da sharar har ta kusa mamaye tituna, a wasu wuraren zaka ga titi ya koma hannu daya yayinda tarin sharar ya mamaye dayan hannun, a wasu wuraren ma sharar ta kashe hanya baki daya ba a iya wucewa, kamar a sabon layi bayan gidan su tsohon Gwamnan Jihar katsina Barista Ibrahim Shehu Shema hanyar ma yanzu babu ita shara ta cike wurin baki daya.
MATSALOLIN DA HAKAN KE IYA HAIFARWA
1. Idan aka yi la’akari da lokacin da ake ciki na damina wanann tarin sharar idan ruwa ya cigaba da bugunta za ta cigaba da rubewa, yayin da hakan zai sa wari ya addabi mutanen da ke makwabtaka da wurin zuba sharar.
2. Na biyu tarin sharar na iya zama wata mafaka ta kwayoyin cutar ka iya haddasa yaduwar cututtuka a cikin al’uma kamar su kwalera, sankarau, kyanda, typoid da sauransu, mun gode Allah bana ba’a samu bullar ko daya daga cikin su ba, Amma barin sharar nan na iya yin sanadin hakan Allah ya kare mu.
3. Shima sauro zai iya amfani da wannan wuri ya cigaba da hayayyafa yana cigaba da haddasa wa jama’a zazzabin malariya.
4. Baya ga kananan yara da dabbobi da a kullu yaumin suke shiga cikin bolar suna tsince tsincen da ka iya haddasa damuwa a cikin al’uma.
Duk da yake bamu san menene dalilin koma bayan wannan hukuma ba, Amma dai abune da Kowa ya saani cewa hukuma irin wannan wadda aikinta ya shafi al’uma Kai tsaye, Kuma aiki na kullum. Lallai tana da bukatar kyakkyawa Kuma ingantaccen shugabanci, tana da bukatar shugaban da yake iya yin amfani da basirarsa da kwarewarsa wajen nemo sabbin dabarun tafiyarda ita ba tare da ya tsaya jiran gwamnati a kowane lokaci ba.
~~~~~~~
Yazid, marubuci kuma mai tsokaci kan al’amuran al’umma, yana rubutu ne daga Birnin Katsina, Najeriya.
~~~~~~~













