SHEIKH ƊAHIRU USMAN BAUCHI: Babban Bangon Musulunci Ya Faɗi
Daga Boss Mustapha

•••••••
A yau Alhamis, 06-07-1447 (Hijiriyya), 27-11-2025 (Miladiyya), al’ummar Musulmi, musamman a Najeriya, sun tsinci kansu cikin babban alhini da jimami saboda rasuwar fitaccen malamin addini, Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi.
Wannan rashi ba ƙarami ba ne, domin Shehi mutum ne wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen yaɗa ilimi, tarbiyya, da fatan alheri ga dukkan al’umma.
Sheikh Ɗahiru malami ne mai jajircewa, wanda ya shafe sama da shekaru 80 yana gina zukata da ilmantar da jama’a. Ya kasance jagora mai gaskiya, mai tausayi kuma mai kyakkyawan hali, wanda duk wanda ya zauna da shi ya amfana. Rayuwarsa ta kasance darasi a kan tsoron Allah, haƙuri, adalci da son zaman lafiya.
Yana daga cikin manyan malamai da suka yi fice wajen karantar da Tafsirin Alƙur’ani mai girma tare da koya wa mutane muhimmancin kyautata zuciya da nisantar zalunci. Kalaman hikima daga bakinsa sun taɓa zukata da yawa, rayuwarsa kuwa ta zama tauraro ga matasa da dattawa.
Rasuwar Sheikh Ɗahiru na tuna mana cewa duniya makaranta ce kuma mutanen kirki irinsa, fitilu ne da Allah ke amfani da su wajen haskaka al’umma. A yau mun rasa fitila amma hasken da ya bari zai ci gaba da haskakawa har tsawon lokaci.
A wannan lokaci mai cike da alhini da tunani, muna miƙa ta’aziyya ga iyalansa, Ɗarikar Tijjaniyya, al’ummar duniya, Najeriya, da dukkanin masu ƙaunar gaskiya.
Sheikh Ɗahiru, fitila ce ta mutu amma haskenta bai mutu ba. Allah ya ji ƙan shi, ya gafarta masa, ya sanya makomarsa ta zama cikin Aljanna Firdausi. Ya kuma ba al’ummar Musulmi haƙuri da ikon karɓar wannan babban rashi. Amin-Summa-Amin!
_______________













