Komawar Kwankwaso Zuwa APC: Gaba Kura Baya Sayaki
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Nan da ɗan lokaci ƙanƙane, ana sa ran Madugun Kwankwasiyya kuma jigo a Jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso zai canja sheka zuwa Jam’iyyar APC mai mulki.
Da ma can a baya, Kwankwaso ya taɓa zama a jam’iyyar APC inda ya bar Jam’iyyar PDP. Sai dai a wannan karon, akwai wasu ƙalubale da ka iya fuskantarsa, a wannan canjin sheƙar.
Wannan ke nuna yadda siyasar Najeriya ke ci gaba da fuskantar juyin-juya hali, musamman yadda manyan ‘yan siyasa ke barin jam’iyya guda zuwa wata a ƙoƙarinsu na samun mafita ko domin kare burinsu na mulki ko tsira daga danniyar siyasa.
Kwankwaso, tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma tsohon Ministan Tsaro, ya taɓa zama cikin Jam’iyyar APC a baya, kuma yana daga cikin waɗanda suka taimaka wajen kafa ta a shekarar 2013 daga jam’iyyun CPC, ACN da PDP. Duk da haka, rikicin gida da rashin jituwa da wasu jiga-jigan jam’iyyar, musamman a Kano da Fadar Shugaban Ƙasa, ya sanya ya fice daga APC zuwa PDP, daga bisani kuma ya kafa NNPP tare da kwashe ɗimbin magoya baya, musamman a Arewacin Najeriya.
A yanzu dai rahotanni na nuna yiwuwar dawowar Kwankwaso cikin APC – lamarin da ke barazana kai tsaye ga rayuwar jam’iyyarsa ta NNPP. Idan Kwankwaso ya koma APC, babu shakka za a iya cewa NNPP za ta ruguje – domin Kwankwaso shi ne ginshiƙi, madugu kuma ruhin jam’iyyar. Ba wani babban jigo da zai iya jan akalarta idan ba shi ba. Wannan zai saka dubban magoya bayansa cikin ɗimuwa da rashin tabbas, domin ɗaki ba ya tashi kuma ragaya ta zauna.
Sai dai kuma, komawarsa APC ba lallai ba ne ta zama mafita. Tarihi ya nuna cewa APC ba jam’iyyar da ke cika ɗaukar masu komawa cikinta da hannu biyu ba, musamman idan ba a yarda da su ba ko kuma ana kallon su a matsayin barazana ga waɗanda ke riƙe da madafun iko. Idan Kwankwaso ya koma APC, akwai yiwuwar a can gaba ya fuskanci matsala, idan amfaninsa ya ƙare, kamar dai yadda ta faru da mutane irin su Malam Nasiru El-rufa’i da Ganduje.
Haka kuma, ko a jiharsa ta Kano, za a iya samun matsala idan ya koma APC. Akwai ɓangaren tsohon Gwamna Ganduje. Akwai manyan masu sha’awar takarar gwamna a 2027, kamar Mataimakin Shugaban Majalisar Zartarwa, Sanata Barau I. Jibrin da Gawuna da sauransu. Haka kuma, shi Gwamna mai ci yanzu a NNPP, Abba Kabir Yusuf, yaya zai yi? Zai bi Kwankwaso zuwa APC ne ko a’a kuma yaya takararsa za ta kasance a 2027?
Shugaba Tinubu, wanda yanzu ke kan mulki, ba zai so wani ɗan siyasa irin Kwankwaso ya dawo ya nemi ɗaukaka ko ya janyo hankalin jama’a fiye da shi ba. Wannan na nufin, komawar Kwankwaso APC na iya zama “gaba kura baya sayaki” – babu tabbas, babu kwanciyar hankali. Kawai zai zama gugar yasa ne, idan an kammala yasar rijiyar 2027, sai a yada ita.
A ɗaya bangaren kuma, idan Kwankwaso ya nace a NNPP, ya ƙi komawa APC kuma ya ƙi shiga cikin Jam’iyyar haɗaka ta ADC ba, akwai barazanar cewa NNPP za ta rasa tasiri a zaɓen 2027. Wannan kuwa saboda jam’iyyar ADC – wacce ke ƙoƙarin kafa wata babbar gwamnatin haɗaka, tana ƙunshe da manyan ‘yan siyasa masu ƙima da tasiri kamar, Atiku Abubakar, Peter Obi, da Malam Nasir El-Rufa’i. Haɗin ƙarfinsu na iya cin karensu babu babbaka, musamman ma idan suka yi nasarar tsayar da ɗan takara mai ƙima da amsuwa ga ‘yan Najeriya.
Don haka, Kwankwaso na cikin mawuyacin hali – idan ya koma APC zai iya fuskantar dannewa da wulaƙanci; idan kuma ya tsaya a NNPP, yana iya rasa gagarumar dama ta siyasa saboda ƙarancin goyon baya da haɗin gwiwa daga sauran manyan ‘yan adawa.
A kowane hali, komawar Kwankwaso zuwa APC na ɗauke da manyan ƙalubale da illoli, da kuma wasu ‘yan fa’idodi masu wuyar samu. Abin da ya rage shi ne dabararsa da ƙwarewarsa su fisshe shi, wajen tantance inda zai fi samun kariya, ɗaukaka da tasiri a siyasar Najeriya. Amma ko ya koma ko bai koma ba, siyasar 2027 za ta buƙaci haɗin gwiwa, hangen nesa, da sabon salo – kuma ga shi lokaci yana ta ƙurewa.
__________
Bashir Malumfashi, shi ne Editan Mujallar Taskar Gizago (online)













