• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Saturday, May 2, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

GOBARA DAGA KOGI: ‘Yan Bindiga Sun Farmaki Fadar Gwamnatin Amurka

• Sun Harbe Sojoji Biyu

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
November 27, 2025
in Babban Labari
0
GOBARA DAGA KOGI: ‘Yan Bindiga Sun Farmaki Fadar Gwamnatin Amurka

Dakarun National Guard a bakin aiki

28
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

GOBARA DAGA KOGI: ‘Yan Bindiga Sun Farmaki Fadar Gwamnatin Amurka

• Sun Harbe Sojoji Biyu

Related posts

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

April 14, 2026
Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

April 8, 2026

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Dakarun National Guard a bakin aiki


                       __________
An rufe Fadar Gwamnatin Amurka (White House), a yayin da wasu ‘yan bindiga suka farmaki fadar, suka yi ta musayar harbi da sojojin da ke gadi, inda har wasu jami’an soja biyu na Rundunar National Guard aka yi zargin sun rasa ransu.

Gwamna Patrick Morrisey a farko ya bayyana cewa sojojin sun rasu, amma daga baya ya ce yana samun “bayanan da ke karo da juna” game da yanayin lafiyar dakarun biyu, inda ya ƙara da cewa, za a fitar da ƙarin bayani idan an tabbatar.

Gwamnan, a shafinsa na X ya bayyana cewa: “Yanzu muna samun bayanai masu karo da juna game da halin da dakarun sojojinmu biyu suke ciki kuma za mu bayar da ƙarin bayani idan mun samu cikakkar hujja.

“Muna addu’a ga waɗannan jaruman dakaru, iyalansu da al’ummar Rundunar National Guard baki ɗaya.”

Rahotanni sun nuna cewa Shugaba Donald Trump yana gidansa na Mar-a-Lago da ke Palm Beach, Florida, a lokacin faruwar lamarin.

A wata sanarwa, sakatariyar yaɗa labaran Fadar White House, Caroline Leavitt, ta ce: “Fadar White House ta samu labari, tana kuma bibiyar wannan mummunan lamari. An yi wa Shugaban Ƙasa bayani.”

’Yan sandan Metropolitan na DC sun ce an kama wanda ake zargi da haddasa harbe-harben.

Dakarun National Guard sun shafe watanni a Washington DC a wani yunƙuri na Trump na ƙarfafa yaƙi da laifuka a babban birnin ƙasar. A shafinsa na Truth Social, Trump ya ce: “Dabban nan da ya harbi sojojin National Guard biyu, waɗanda duk suna cikin hali mai tsanani, suna kwance a mabanbantan asibitoci; shi dabban ya jikkata sosai kuma duk da haka, zai fuskanci mummunan hukunci.”

Sharhi:
Wannan lamari, shi ake kira gobara daga kogi, wai maganinta Allah. Kuma hakan ke nuna mana cewa ashe lamarin taɓarɓarewar tsaro ba ga Najeriya ne kaɗai ba, har da manyan ƙasashe, irin Amurka, wacce ake gani kamar giwar duniya.

Wannan lamari ya faru ne fa, a daidai lokacin da Shugaba Donald Trump yake bugun ƙirji da barazanar cewar zai farmaki Najeriya, saboda taɓarbarewar tsaro. Kodayake shi a nasa batun, akwai son zuciya a ciki, inda ya yi ƙazafin cewa Kiristoci kaɗai ake yi wa kisan-ƙare-dangi a Najeriya. Kowa kuma ya san ba haka ba ne.

A yanzu da balahirar guguwar rashin tsaro ta farmaki Fadar Amurka, to yaya ke nan! Anya kuwa mai bunu a gindi, yana da zarafin kai wa wani gudunmawar kashe gobara?

Gare ku jama’a: Yaya kuke kallon wannan lamari? Ku bayyana a Comment Section.
__________

Previous Post

SHEIKH ƊAHIRU USMAN BAUCHI: Babban Bangon Musulunci Ya Faɗi

Next Post

Jama’a Mu Fahimta: Musulunci Daban Ƙungiyanci Daban

Related Posts

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Babban Labari

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

April 14, 2026
Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume
Babban Labari

Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

April 8, 2026
Yadda Babban Jigon Jam’iyyar APC Daga Kano Ya Mutu A Otel
Babban Labari

Yadda Babban Jigon Jam’iyyar APC Daga Kano Ya Mutu A Otel

April 2, 2026
Next Post
Jama’a Mu Fahimta: Musulunci Daban Ƙungiyanci Daban

Jama'a Mu Fahimta: Musulunci Daban Ƙungiyanci Daban

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

GA ZAKARU 20:  NA GASAR RUBUTUN GAJERUN LABARUN HAUSA TA GIDAUNIYAR ZANNA-WALI (2025)

GA ZAKARU 20: NA GASAR RUBUTUN GAJERUN LABARUN HAUSA TA GIDAUNIYAR ZANNA-WALI (2025)

January 23, 2026
Justice For Walida: A Call on Jigawa State Government to Take Urgent Action and Secure the Release of Walida Abdulhadi

Justice For Walida: A Call on Jigawa State Government to Take Urgent Action and Secure the Release of Walida Abdulhadi

February 24, 2026
Jan Hankali Ga Matasan Soshalmidiya

Jan Hankali Ga Matasan Soshalmidiya

July 11, 2023
Najeriya 2027: Matsalolin Da Za Su Iya Wargaza Takarar Obi Da Kwankwaso

Najeriya 2027: Matsalolin Da Za Su Iya Wargaza Takarar Obi Da Kwankwaso

March 29, 2026

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana
  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)
  • General Buratai (A Poem)

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

April 28, 2026
Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

April 27, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.