GOBARA DAGA KOGI: ‘Yan Bindiga Sun Farmaki Fadar Gwamnatin Amurka
• Sun Harbe Sojoji Biyu
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
An rufe Fadar Gwamnatin Amurka (White House), a yayin da wasu ‘yan bindiga suka farmaki fadar, suka yi ta musayar harbi da sojojin da ke gadi, inda har wasu jami’an soja biyu na Rundunar National Guard aka yi zargin sun rasa ransu.
Gwamna Patrick Morrisey a farko ya bayyana cewa sojojin sun rasu, amma daga baya ya ce yana samun “bayanan da ke karo da juna” game da yanayin lafiyar dakarun biyu, inda ya ƙara da cewa, za a fitar da ƙarin bayani idan an tabbatar.
Gwamnan, a shafinsa na X ya bayyana cewa: “Yanzu muna samun bayanai masu karo da juna game da halin da dakarun sojojinmu biyu suke ciki kuma za mu bayar da ƙarin bayani idan mun samu cikakkar hujja.
“Muna addu’a ga waɗannan jaruman dakaru, iyalansu da al’ummar Rundunar National Guard baki ɗaya.”
Rahotanni sun nuna cewa Shugaba Donald Trump yana gidansa na Mar-a-Lago da ke Palm Beach, Florida, a lokacin faruwar lamarin.
A wata sanarwa, sakatariyar yaɗa labaran Fadar White House, Caroline Leavitt, ta ce: “Fadar White House ta samu labari, tana kuma bibiyar wannan mummunan lamari. An yi wa Shugaban Ƙasa bayani.”
’Yan sandan Metropolitan na DC sun ce an kama wanda ake zargi da haddasa harbe-harben.
Dakarun National Guard sun shafe watanni a Washington DC a wani yunƙuri na Trump na ƙarfafa yaƙi da laifuka a babban birnin ƙasar. A shafinsa na Truth Social, Trump ya ce: “Dabban nan da ya harbi sojojin National Guard biyu, waɗanda duk suna cikin hali mai tsanani, suna kwance a mabanbantan asibitoci; shi dabban ya jikkata sosai kuma duk da haka, zai fuskanci mummunan hukunci.”
Sharhi:
Wannan lamari, shi ake kira gobara daga kogi, wai maganinta Allah. Kuma hakan ke nuna mana cewa ashe lamarin taɓarɓarewar tsaro ba ga Najeriya ne kaɗai ba, har da manyan ƙasashe, irin Amurka, wacce ake gani kamar giwar duniya.
Wannan lamari ya faru ne fa, a daidai lokacin da Shugaba Donald Trump yake bugun ƙirji da barazanar cewar zai farmaki Najeriya, saboda taɓarbarewar tsaro. Kodayake shi a nasa batun, akwai son zuciya a ciki, inda ya yi ƙazafin cewa Kiristoci kaɗai ake yi wa kisan-ƙare-dangi a Najeriya. Kowa kuma ya san ba haka ba ne.
A yanzu da balahirar guguwar rashin tsaro ta farmaki Fadar Amurka, to yaya ke nan! Anya kuwa mai bunu a gindi, yana da zarafin kai wa wani gudunmawar kashe gobara?
Gare ku jama’a: Yaya kuke kallon wannan lamari? Ku bayyana a Comment Section.
__________













