TSOKACINMU NA YAU (24)
Yau Litinin, 21-Ramadan-1446, Hijirar Manzon Allah (saw), wacce ta yi daidai da 24-Maris-2025, Miladiyya.
Girman kai rawanin tsiya, inji masu hikima. Yau shi ne taken tsokacinmu.
Ya ku ‘yan uwa, babu shakka a gaskiyar masu hikima, domin kuwa shi girman kai, ba rawani ne na tsiya ba kaɗai, shi ne fandeshin duk wata asarar ta duniya da lahira.
Idan muka duba tarihi, girman kai shi ne babban dalilin taɓewar shaiɗan, wanda shi ne halitta na farko da ya fara yi wa Allah girman kai; ya ƙi bin ummurninSa na yi wa kakanmu Annabi Adamu (as) sujada. Dalili ke nan ya zama taɓaɓɓe, asararre a dukkan rayuwar duniya da lahira, har gaba da abada.
‘Yan uwa, mu guje wa girman kai, don mu tsira a rayuwar duniya da lahira.
Allah sa mu dace, Amin.
Mu wuni lafiya.
Naku,
Bashir Yahuza Malumfashi,
Editan Mujallar Taskar Gizago.












