TSOKACINMU NA YAU (26)
Yau Laraba, 26-Ramadan-1446, Hijirar Manzon Allah (saw), wacce ta yi daidai da 26-Maris-2025, Miladiyya.
‘Yan uwa, tsokacinmu na yau, takensa shi ne, ka koyi ɗabi’ar tambaya da ƙwanƙwasa ƙofa a rayuwa.
Ina hikimar haka? A lokacin da kake buƙatar wani abu a rayuwa, lallai ne sai ka tashi tsaye domin neman shi. Wannan abin yana nan a rufe a wani wuri, sai ka ƙwankwasa ƙofar sannan za a buɗe maka kafar shiga, domin ka ɗauko shi.
Ka ƙwanƙwasa ƙofar ƙasa, domin noman abinci, ƙofar makaranta domin neman ilimi, ƙofar kasuwa domin neman kuɗi – haka ma sauran al’amuran rayuwa. Ka sani, zomo ba ya kamuwa daga zaune, in ji masu hikima.
Tambaya kuwa, an ce rabin ilimi ce. Allah Ya faɗa a Alkur’ani, “Ku tambayi masana domin sanin abin da ba ku sani ba.” Da tambaya ne ake sani kuma a ƙaru a rayuwa.
Allah sa mu dace, Amin.
Mu wuni lafiya.
Naku,
Bashir Yahuza Malumfashi,
Editan Mujallar Taskar Gizago.













