Daga Bashir Yahuza Malumfashi
Auren Al-Amin Ciroma Da Wasila Isma’il: Kira Na Musamman Ga Dattawan Kannywood
Na yi baƙin ciki matuƙa da ganin labarin abokinmu kuma ɗan uwa, Al-Amin Ciroma da uwargidansa Wasila Isma’il, inda Mujallar Fim ta ruwaito cewa auren nasu, wanda ya rayu tsawon shekara 21 ya kawo ƙarshe.
Bisa ga wannan, nake ganin ya dace in gayyato wasu daga cikin Dattawan Kannywood, domin su haɗa hannu su bi al’amarin, yadda za a kawo gyara da sasanci tsakanin ma’auratan.
A nan, zan ambaci kaɗan daga irin waɗannan manya, domin ganin an samu fa’ida cikin sauƙi. Waɗannan kuwa su ne, Alhaji Hamisu Lamiɗo Iyan-tama da Yakubu Lere da Ibrahim Sheme da Ado Ahmad Gidan Dabino da Ibrahim Mandawari.
Ya ‘yan uwa, don Allah kuma don ƙaunar sunnar Manzon Allah (saw), ku haɗa hannu ku ceto wannan aure. Ku yi ƙoƙari ku sasanta waɗannan ma’aurata, waɗanda tsawon shekaru 20, tun da suka yi aure ake doka misalin abin kirki da su.
A duk lokacin da wani ɗan fim ko ‘yar fim ta yi aure, akan yi masu fatan alheri da cewa Allah sa su yi koyi da auren Al-Amin Ciroma da uwargidansa Wasila Isma’il, waɗanda suka jure zama da juna, da daɗi ba daɗi.
To yau da rana tsaka, a ce wannan aure da ya samar da ingantattun ‘ya’ya biyar, maza da mata ya mutu, babu shakka ba abin daɗi ba ne.
A ɓangaren abokinmu, Malam Al-Amin Ciroma kuwa, ina kira gare ka, a yadda na san ka a mutum mai haƙuri da juriya, don Allah ka yi haƙuri, ka ba da ƙofar sasanci da matarka, domin kare martabarka da ta iyalinka masu albarka.
Idan na jiyo kan uwargida Wasila Isma’il, ke ma mun san ki da mutunci, mun san ki da hangen nesa. Don Allah ki kai zuciya nesa, ki yi haƙuri, ku zauna ku ƙara nazari, ku samar da kafar sasanci da yafiya a tsakaninku. Ku daure ku farfaɗo da soyayyarku da ƙaunar junanku, ku koma aure. Ko domin martaba da mutuncin ‘ya’yanku.
Ina roƙon Allah Ya kunyata Shaiɗan, Ya daidaita wannan al’amari. Amin.
~~~~~~~
Ni ne ɗan uwanku,
Bashir Yahuza Malumfashi.
~~~~~~~












