TSOKACINMU NA YAU (11)
Yau Talata, 11-Ramadan-1446, Hijirar Manzon Allah (saw), wacce ta yi daidai da 11-Maris-2025, Miladiyya.
Ga tsokacinmu na yau:
“Ya ku ‘yan uwa, a yau nasiha za mu yi wa juna kamar yadda muka saba. Mu lizimci gudanar da rayuwarmu daidai da samunmu.
Ma’ana, kamar ta azancin maganar Hausawa, daidai ruwa daidai ƙurji. Ko kuma kamar yadda suka ce, mu guji wuce makaɗi da rawa. Idan ba ki da gashin wance, kada ki ce sai kin yi kitso irin na wance. Domin idan ka daka rawar wani, za ka rasa turmin daka taka rawar.
Mu zamo masu gode wa abin da Allah Ya ba mu.”
Allah sa mu dace, Amin.
Mu wuni lafiya.
Naku,
Bashir Yahuza Malumfashi,
Editan Mujallar Taskar Gizago.












