TSOKACINMU NA YAU (10)
Yau Litinin, 10-Ramadan-1446, Hijirar Manzon Allah (saw), wacce ta yi daidai da 10-Maris-2025, Miladiyya.
Ga tsokacinmu na yau:
“Ya ku ‘yan uwa, ku zo mu yi wa juna nasiha game da MUTUNTA JUNA. Ganin mutunci da girmama juna haƙƙi ne na Kowane ɗan Adam. Allah Ya ce ya karrama bani Adama. Ke nan ya zama wajibi mu karrama juna, muddin dai muna son mu ji daɗin tarayya da juna.
Kowane mutum yana da ra’ayi da aƙida, kuma kowa yana da abin da yake so da wanda ba ya so. Don haka mu zamanto masu kare ra’ayoyi da haƙƙoƙin juna dangane da abin da ya shafi addininmu, al’adunmu da fahimtarmu, sai mu zauna cikin lumana da juna.
Mu riƙa kiyaye duk wata gardama marar amfani, wacce za ta kawo mana saɓani da juna. Mu riƙe mutuncinmu, mu mutunta juna, yadda wasu za su mutunta mu.”
Allah sa mu dace, Amin.
Mu wuni lafiya.
Naku,
Bashir Yahuza Malumfashi,
Editan Mujallar Taskar Gizago.













